Wednesday 3 July 2013

Mene Ne Adabin Kasuwa?

MENE NE ADABIN KASUWA? Tare da Bashir Abusabe Kamar yadda muka sania rayuwar adabin Hausa ta biyo zanguna mabambanta, wannan ba sai an yi dogon sharhi ba, domin kuwa daga tashin Hausawa na zaman gargajiya har zuwa lokacin da suka cudanya da baki an sami sauye-sauye da adabin Hausawa ya yi ko dai ta fuskar sauyawar riga daga ta gargajiya zuwa ta zamani (Larabci ko Ingilishi ko Faranshi) ko kuma ta sauyawar kayan cikin adabin saboda haduwa da sababbin ladubban rayuwa . Irin sauye-sauyen da aka samu daga gargajiya zuwa zamani abu ne da masana sun sha ambaton sa, kila abin da ba a fi mayar da hankali kai sosai ba shi ne yadda gwamutsuwa da bakin al’amurra ke haifar da sababbin batutuwa da ke bukatar kara bincike da nazari. Batutuwan da suka yi tashe a cikin ‘yan shekarun nan, musamman abin da ya shafi kagaggun labaran Hausa, bai wuce batun nan na Adabin Kasuwar Kano ba, wato littattafan da yawancinmu ke kira Labaran Soyayya da suka tuzgo daga sassa daban-daban na kasar Hausa da ke hedikwata a birnin Kano. Samuwa da watsuwa ko kuma karbuwa da kuma ce-ce-ku-ce da wannan sabon salon adabi ya samu kansa a ciki, tsakanin marubuta da manazarta da masana a kasar Hausa da ma sassan duniya daban-daban ya jawo ayyukan nazari da musayar miyau mai tarin yawa. Abin da za mu yi kokarin yi a nan shi ne shimfida tabarmar nazari game da wannan fage ta hanyar neman sanin yadda adabin kasuwa yake ta hanyar tambayar ko akwai wani abu wai shi adabin kasuwa? Idan akwai shi to a yaya yake? Shin ana iya samun sa a kasashe masu tasowa kamar Nijeriya? Ko kuwa dai wanda ake da shi da ake kira Adabin Kasuwar Kano, an sa masa sunan ne domin cin mutunci da batunci ko son rai? Abin da za mu sa gaba bai wuce amsa wadannan da ma wasu tambayoyi da ka iya biyo baya ba, ta haka kila haske ya karu game da wannan fage na tarihin adabi da zai bayyana mana bambancin da ke tsakanin adabi na zahiri da wanda ake kira na kasuwa da kuma yadda irin fasali ya samu ginuwa a kasar Hausa. Yanayin Gangariyar Adabi Da Adabin Kasuwa A duk lokacin da aka soma batun da ya shafi Adabin Kasuwa abubuwa da dama ke zuwa zuciyar mai nazari ciki kuwa har da tunanin nan da ke nuni da cewa idan har akwai adabin kasuwa to ke nan ashe akwai wani adabin da ba na kasuwa ba. Idan kuma ka dauki ma’anar Adabin Kasuwa a luggance da ke nufin adabi na kowa da kowa ko na yayi ko abin da ke jan hankalin jama’a a kodayaushe, ke nan ana iya cewa akwai adabin da ke da akasin haka, ma’ana adabin da ba na kowa da kowa ba, adabin manya, masu ilmi ko sarauta ko daraja a tsakanin al’umma, a takaice dai adabin da ke shimfide a wani wuri domin manazarta da masana ko kuma wanda fagensa ba na kowane dan tagaja-tagaja ba ne wajen saye da karantawa da nazari, wato abin da ake wa lakabi da gangariyar adabi. Saboda haka kokarinmu a nan shi ne mu bambanta tsakanin gangariyar adabin da wanda ake wa lakabi da na kasuwa, domin ta haka ne za a gane yadda tunanin samuwar Adabin Kasuwar Kano ya tusgo, yake kuma gudana. Adabi dai kamar yadda masana suka yi nuni, kundi ko hoto ko madubi ne, (dubi Dangambo, 1984, da Gusau, 1995 da Malumfashi, 2002) da ke dauke ko nuna hanyar gudanar da rayuwar al`umma. Za a iya fahimtar irin wannan adabi ta yin la`akari da abubuwa guda biyu; Na farko shi ne harshen da ake amfani da shi, wanda yake makunshin tarihi, kuma linzamin bayyana tunani ko kuma wata manufa. Na biyu kuma ita ce fasaha, wadda ita ke bayyana tunanin da ke cikin zuciya a aikace, kamar yadda Muhammad, (2001) ya bayyana. Shi kuma Cuddon,(1999) da yake kokarin fitar da ma’anar adabi a luggance, cewa ya yi adabi na iya kasancewa abubuwa da dama da suka hada da wasan kwaikwayo da waka da gajerun labarai da rubutattun litattafai da dai sauransu. Ya ci gaba da cewa idan har aka ce wannan aikin adabi ne, to makunshiyar aikin ta bambanta da sauran kwashe-kwashe na yau da kullum, musamman idan abin ya shafi gaskiyar lamari ko kuma fadar tarihi, ke nan adabi yana da wasu siffofi da suka bambanta shi da wasu ayyuka da ba su da tasiri irin nasa. Duk da haka akwai ayyuka ko rubuce-rubuce da dama wadanda ba a yi su don su kasance na adabi ba ne, amma kuma za a iya sanya su cikin aikin adabi; saboda ingancin aikin da asalinsa ko kuma irin kyawo da kuma fasahar da aka nuna wurin rubuta shi, kamar yadda (Cuddon, 1999) ya nuna. Daga wannan hasashe za a iya cewa adabin da ke da wadannan siffofi da aka ambata a sama, shi ne ke kasancewa gangariyar adabi, akasin haka kuma sai ya zama wani abin, kila ma na kasuwa ko kuma gwanjo ko makamancin haka. Kamar yadda kowane sashe na duniya yake da gangariyar adabi, to haka a wasu sassan duniya ake da adabin kasuwa, (Market Literature) ko kuma adabin yayi (Popular Literature). To amma idan muka ce adabin kasuwa, nan zai iya kasancewa na yayi, domin kuwa duk abu daya suke tattaunawa. Duk abin da ya kasance na kasuwa to yana da alaka da yayi. Kasuwa dai wuri ne da ake saye da sayarwa na dukkan abubuwan rayuwa, duk wanda ke cikin wannan al`umma yana iya zuwa cikinta domin yin kasuwancinsa. Saboda haka adabin kasuwa wani bangare ne na adabin al’umma da kowa zai iya shiga cikin kogin ya yi iyo ko kurme; masani ko malami ko manazarci ko akasin haka. Ke nan irin wannan adabi wani abu ne ko dai waka ko wasan kwaikwayo ko kananan labarai, ko rubutattaun litattafai da aka tsara a wani zangon rayuwar jama’a, ake kuma tsintar su a tsakanin jama’ar ba tare da wani kandagarki ba. Ta fuskar sayar da su ba a yi wani tanadi na wurin da ya dace ba, ko dai a same su a kasuwa ko wurin hirar matasa ko tsakanin matan aure ko makarantu ko kuma ma duk inda jama’a ke tururuwa domin karatu da rubutu. Haka kuma idan aka ce adabi na yayi ne ana nufin cewa zai rayu daga wani lokaci zuwa wani, wato akwai lokacin da yake tashe, akwai kuma lokacin da yake sallacewa, sai a bar masana da yin rubdugu kansa, (Malumfashi, 2002). Sai dai ya kamata a lura cewa akwai lokutta kuma da ake kallon irin wannan adabin na kasuwa ko yayi a matsayin adabin talakawa ko marasa shi, wato ya kebanta ne ga wasu gungun jama’a a cikin wani zamani da ba su damu da adabin da ke gudana ba, kila ko don ba su da kudin sayen sa ko kuma ya kasance na masu gari. Idan aka fadada tunani a nan za a ga cewa shi wannan adabi na kasuwar ko yayin, saboda canzawar zamani ta sa ake masa wani sabon kallo, musamman da yake ba a damu sosai da yi masa gangariyar nazari ba. Kai ba wannan ba ai masana da dama ba su dauki aikin adabi irin wannan abin tokabo ba, shi ya sa ba a damu da sanin inda ya sa gaba ba. Sai dai ko da aka soma nazarin nasa daga baya, an kuma shigo da ayyukan adabi da mutum na iya cewa ba irin na adabin kasuwa ko yayin da aka saba ji da gani ba ne. A halin yanzu daga cikin ayyukan adabin kasuwa ko na yayi da ake da su an sanya irin kagaggun labaran da a da ba su cikin irin wannan rukuni, wato irin wadanda suka hada da labaran bincike ko tsafi ko na ban tsoro ko soyayya ko na Amurkawan dauri ko na ban dariya ko kimiyya, wato dai kagaggun labarai da milyoyin jama’a ke saye da karantawa a sassan duniya daban-daban ko da kuma ba a nazarin su a ajin adabi ko jami’o’i, musamman daga shekarun 1930. Har yau takaddama ba ta kare ba dangane ko wadannan irin ayyukan adabi na gangariyar adabi ne ko kuma kwamacala. Ga masana kamar yadda aka bayyana a (eNotes.com), irin wannan aikin adabi na kasuwa bai da nasaba da aikin kwarai, ana nuni da cewa dabara ce kurum ta samun kudi da suna, amma ba adabin da za a ta da jijiya wajen karatu ko nazari ba ne. Fasalin Adabin Kasuwa A Duniya Daga nazarin da aka gudanar an fahimci cewa adabin kasuwa ko na yayi yana tafiya ne kafada da kafada da gangariyar adabin al’umma. Shi gangariyar adabin yana kasancewa ne tsakanin masu ilmi ko hannu da shuni ko kuma iyayen kasa. Duk wani abu da ba na wannan gungun mutane ba, yawanci shi ake wa lakabi da adabin kasuwa ko yayi. Alal misali kusan duk yawancin ayyukan adabi da suke da wannan siffa a Turai ko Amurka ko sauran sassan duniya an samar da su ne tsakanin karni na 16 da 17 da na 18, daidai lokacin da fasahar dab’i ko buga littattafai ta yi tashe a duniya. Kamar yadda bayanai suka yi nuni , yawancin jama’a da masana idan ana maganar adabin karni na 16 da 17 da na 18, ana maganar gangariyar adabi ne ko na masu ilmi ko mulki ko dukiya, amma ba su kadai ne suka kwashi nasu kason ba daga rayuwar adabi, akwai adabin talakawa ko na kasuwa, wato na kowa da kowa. Ma’ana, an samar da adabin da aljihun talaka zai iya biya, ya saya don karantawa. Wannan dama ta samu ne domin an samar da injinun buga littattafai na bakin hanya da suka ba talaka damar ya sami gurbin da zai buga nasa adabin. Ire-iren wadannan ayyukan adabin su ne ake ba sunaye daban-daban da suka hada da Grub Street Literature ko Chapbooks. Wadannan lakabobi sun wanzu ne saboda la’akari da irin yadda aka samar da adabin ko wuraren da ake samar da littattafan ko kuma yanayin buga da sayar da su. Su dai Grub Street Literature su ne ayyukan adabin da aka samar daga wuraren buga littattafai da ke kan Titin Grub a Landon. Da yake a tsakanin karni na 16 da 17 da na 18 an samar da marubuta na kwarai, sai dai rubutun nasu ya fi mayar da hankali ne ga masu-fada-a-ji, bai ta’allaka ga sauran jama’a ba, ga shi kuma sun fi sauran jama’ar yawa, wannan ya sa aka shiga neman wasu da za su agaza da nasu rubutun. Sai dai yawancin irin wadannan marubuta ba su da sanayya ta zamani game da fasahar rubutu da kaga labarai, shi ya sa idan sun yi rubutu ake biyan su kudade kadan, wannan ya sa suke rayuwa a cikin talauci da kunci. Shi kansa inda suke zama a bakin titin domin yin aikin nasu na adabi, wuri ne na kazanta da yawan lalata da tashin hankali; nan ake samun barayi da mabarata da dai ire-irensu; nan ne marubutan da injinan buga ayyukansu suka daura aure. Su kuwa Chapbooks littattafai ne da ake wa lakabin littattafai masu arha, su ne ayyukan adabin da suka kasance na yayi ko na jama’a a karo na farko a wancan zamani na karni na 17 da 18. Ba ruwansu da kamfanonin hukuma ko na gwamnati, ba kuma ruwansu da manyan kamfanonin dab’i da ke neman kazamar riba. Ana kuma shirya da buga irin wadannan littattafai domin isar da sako ga talakawa ko masu sha’awar adabi, amma ba su da kudin sayen gangariyar adabin da ke wanzuwa a lokacin. Wannan damar ce marubutan da masu karatu ke amfani da ita domin su isar da sako ga sauran jama’a ba tare da kamfanin dab’i ya sa baki ba, yawancin abubuwan da ake samarwa sun hada da wake-wake da labarai da ayyukan addini da sakonnin siyasa da makamantansu. Tarihi ya nuna cewa ko da hada-hadar dab’i da rubuce-rubuce ta kankama daga karni na 15 da na 16 akwai ire-iren wadannan ayyuka masu arha, yawancinsu sun fita kasuwa ne daga karni na 17 da na 18 a Ingila, an nuna cewa sun kai kokoluwa ne a shekarar 1775, ta yadda ake samar da littattafai sama da 200,000 a kowace shekara. Wadannan littattafai sun taimaka wajen raya ayyukan adabin Ingila a wancan lokaci, sun sanya son karatu ga wadanda ba su yi nisa a karatun ba, ko suka yi karatun suka watsar daga baya. Yawancin wadannan littattafai ba su da yawan shafi, ba a yi musu bugun kwarai, sa’annan ana sayar da su da arha, daga wannan titi zuwa wancan, a maimakon wuraren da aka tanada domin sayar da gangariyar adabi. Domin ganin yadda wannan fasali ya kasance, bari mu dubi yadda na zamanin Elizabeth ya kasance a Ingila. Adabin Kasuwar Sarauniya Elizabeth A Ingila Da yake mun ga yadda wannan adabi ya kasance da kuma tasirin da ya yi tsakanin al’umma a Ingila, zai dace a nan mu fadada kan wannan batu domin mu ga yadda fasalin adabin kasuwar ya kansance ta hanyar bayar da misalai. Da yake tun da farko mun yi nuni da cewa harkar ta adabin kasuwa ta samo tushe ne daga Ingila, ya dace mu fahimci yadda al’amarin ya kasance, kafin mu shiga wasu sassan na duniya mu ga su kuma irin nasu fasalin. Daga nazarin da aka yi an fahimci cewa akwai bambance-bambancen da aka samu a tsawon zamanin aikin adabin Ingilishi, tunanin farko dai ya fara ne daga `yan Sukotlan ba daga Ingila ba, shi wannan adabin ne ya ci gaba da watayawa a tsakanin karni na goma sha biyar zuwa farko, da tsakiyar karni na goma sha shida. Wannan ne ya samar da gagarumin aikin Tottel a shekarar 1557. Shi dai wannan littafin ya shahara ne saboda dalilai da dama; Na farko dai abin da ya fi jan hankalin sababbin makaranta a wannan lokacin shi ne mafi yawan abin da littafin ya kunsa abu ne wanda ba a san da shi ba ba, haka kuma akwai hasashe ba yakini ba a cikin labarin, wanda kuma wannan shi ya fi burge masu karatun ayyukan adabin wannan lokacin, ba kamar ayyukan wasu da suka wallafa ba wadanda ko dai sun mutu ko kuma sun dade kwarai da yin rubutun, (Saintsbury,1920). Wannan zamani na Sarauniya Elizabeth kamar yadda muka yi bayani akwai aikin manyan masana a kasar Ingila, kamar fitaccen marubucin nan na wasan kwaikwayo, Christopher Marlowe da marubuta wakoki irin su Edmund Spenser, da kuma shahararrun masana kimiyya irin Francis Bacon. Marubuta da dama na wannan lokacin sun ji dadin yadda `yan majalisar Sarauniya ke amsar su in sun kai ziyara, duk da cewa suna daga cikin talakawa, (Saintsbury, 1920). Wannan kuwa ya faru ne domin tun farkon mulkin Sarauniya Elizabeth, ita ta kasance tamkar Uwar kungiyar, kuma mai bada taimako ga marubuta labaran wasan kwaikwayo, kai har aiwatar da wasan kwaikwayon ake yi a gabanta. A shekarun 1560 aka fitar da wasan Kwaikwayo na Blank Verse Tragedies, wanda za a iya cewa shi ne ya bude kofa wurin samuwar kimiyyar wasan kwaikwayon da ake nazari har zuwa yau. A shekarar 1568 ne aka aiwatar da wasan kwaikwayon a gaban sarauniya a bisa dandamali. Irin yadda aka samar da litattafai da ayyukan adabin Elizabeth ya taimaka kwarai wurin ceton adabin Ingilishi daga shiga cikin hadari na kwasar ayyukan da ‘yan kasuwa suke yi, wadanda kuma ake samarwa da tsada. Misali, a lokacin da Tottel ya fiddo littafin shi na Miscellany ba dukkan mawallafa na lokacin suka san da wannan hanyar ta fiddo da littafin kai tsaye ba, wato ba tare da an mika shi ga masu wallafar zamani ba, (Saintsbury,1920). Ta bangaren rubutun zube ma, lokacin mulkin sarauniya Elizabeth ya samu tagomashi sosai, saboda a lokacin ne aka samu ayyukan adabi wadanda suka yi tashe ko kuma suka zama na yayi, domin a lokacin malaman da ke koyarwa a Jami`ar Kambirij (Cambridge) sun taimaka kwarai da gaske wurin samar da ayyukan masana irin su Ascham da Wilson, da sauransu ta fuskar zube. Duk da cewar akwai ayyukan magabata irin su Thomas Hoby, amma dai za a iya cewa Roger Ascham shi ne ya fara bude fagen da littafinsa Toxophilus da ya rubuta aka kuma wallafa shi a shekarar 1545, amma dai littafinsa da ya fi tashe, wato Schoolmaster bai fito ba sai bayan da ya mutu, (Saintsbury,1920). Shi dai Ascham fitacce, kuma shahararren malami ne domin har sarauniyar Ingilar ma sai da ya koyar da ita a makaranta. Kamar yadda muka gani a sama, Adabin Elizabeth na Ingila ya ratsa zangunan mabambanta. Misali, mun dai ga cewar akwai ayyukan adabi da aka yi kafin lokacin Elizabeth din kamar na su Thomas More wanda ya yi rubuce-rubuce, musamman na wakoki da kuma Wyatt da sauransu. Ko a lokacin mulkin Sarauniya Elizabeth din ma, ayyukan adabi da suka fi tashe su ne wakoki da wasan kwaikwayo da kuma kagaggun labaran, amma dai masu sarrafa wakokin da wasan kwaikwayo sun fi yawa da tashe, wato kamar masana irin su Edmund Spenser da sauransu, (Saintsbury,1920). A bangaren wasan kwaikwayo da kagaggun labarai kuwa dole ne masana irin su Shakespeare su shige gaba, sannan ga Marlowe wanda zakakuri ne, wanda ayyukansa suka yi tashe, ga kuma Ben Jonson wanda ya kwaikwayi ayyukan magabatansa, ya samar da nasa. Ta bangaren kagaggun labarai kuwa akwai marubuta irin su Philip Sidney da Richard Hakluyt da Francis Bacon da sauransu da dama. Daga wannan takaitaccen bayani mun fahimci cewa a kasar Ingila ne aka samar da wannan fasali na adabin jama’a ko na kasuwa, mun dai fahimci cewa irin wannan adabi na yayi ko kasuwa ya wanzu tsakanin karni na 16 da na 17 lokacin da adabin sarauniya Elizabeth ya yi tashe tsakanin shekarar 1558 zuwa 1603. Shi dai adabin Elizabeth ba yana nufin ita Sarauniyar ce ta wallafa ko buga shi ba (kodayake ita ma ta jefo wakokinta da aka karanta, musamman On Monsiuer’s Departure), sai dai ana iya cewa a lokacin mulkinta ne aka samar da yawancin ayyukan adabin da ake wa lakabi da na yayi ko kasuwa, duk kuwa da cewa ayyuka ne na kwarai. Abin da ya sa wannan gangariyar adabi ya kasance adabin kasuwa shi ne ya samu karbuwa a hannun yawancin jama’ar Ingila a cikin kankanen lokaci, (Wikipidia.org). Duk da cewa akwai kagaggun labarai cikinsa, abin da ya fi yin tashe shi ne wasan kwaikwayo da wakoki. Adabin Elizabeth ya somo ne daga zamanin su Tottel da suka wanzu da wakokinsu zuwa masu tsara labarai na zamanin Caroline, (Saintsbury,1920). Ba wani abu ya sanya wannan zamani ya kasance na ayyukan adabin al’umma ba sai ganin manyan mashahuran marubutan da suka yi tashe a wancan zamani sun wanzu ne a lokacin, kuma har yau suna tashe a fagen nazari da sharhi. Akwai marubuta ayyukan adabi da suka hada da William Shakespeare da Christopher Marlowe da Ben Johnson da Edmund Spencer da John Fletcher da Thomas Kyd da Thomas Middleton da Thomas Nashe da John Webster da John Donne da Philip Sidney da sauransu, duk a wannan zamani suka wanzu. An kira wadannan mutane da ayyukan adabinsu a matsayin na yayi a wancan lokaci, saboda sun kasance mutane ne ko kuma ayyukansu da jama’a ke rububi. Sa’annan kuma yawancin ayyukan nasu kwafe-kwafe ne ko dai daga wasu can da aka yi a baya da suka shahara ko kuma tsakanin marubutan wannan zamani. Misali, Thomas Kyd da aikinsa na The Spanish Tragedy, shi ya ba Shakespeare hasken rubuta Hamlet, ba kuma nan kadai Shakespeare ya tsaya ba, ya shiga cikin taskar tarihin zamanin da, da kuma zamanin da ya rayu ya kwafo abubuwan da suka taimaka ya gina nasa adabin. Bincike ya nuna cewa wakokin Sonnet da Thomas Wyatt ya kaddamar su ne kuma Shakespeare da wasu na zamaninsa suka ci gaba da tallatawa, kuma sun ja ra’ayin Thomas Campion wanda ya rubuce su a takarda, aka shiga rububinsu a gidajen al’ummar wancan zamani, (Wikipidia.org). Ke nan ba kamar yadda ake tunani ba, yawancin ayyukan adabin zamanin Sarauniya Elizabeth ta 1, ba wai rashin kyau ko ma’ana ko kuma rashin goyon bayan hukuma ba ne matsalar da ta sa aka kira su na yayi, ba kuma domin ana rubutun domin talakawa ba ne kadai, sai dai domin yanayin samuwarsu, wato yadda jama’a ke ta wawason su da kuma shiga cikin harkar saye da karantawa da rubutawa, ciki har da masu gari, Sarauniya. Babban abin da ya fi fitowa fili game da wannan zamani shi ne yadda gamade da kwashe-kwashen ayyukan wasu ke taimakawa wajen gina sabon adabin da ya burge al’ummar wancan zamani. Saboda haka daga abin da aka tattaro dangane da adabin Sarauniya Elizabeth na Ingila mu iya cewa mafi yawan ayyukan adabi na kwarai, an samar da su ne a wannan lokaci, cikin wadannan shekarun ne aka samar da rubuce-rubucen adabi, musamman abin da ya shafi zane da wakoki, wasan kwaikwayo da sauransu. Adabin Kasuwar Kitsch a Jamus Duk da an ce samuwa da ginuwa na adabin jama’a ko yayi ya tusgo ne daga kasar Ingila, amma ba a kasar Ingila irin wannan rayuwar adabin kasuwa ko yayi ya samu gindin zama ba kawai, a can Jamus a cikin karni na 18 da na 19, an sami irin wannan adabi da ake wa lakabi da Kitsch. A cikin harshen Jamusanci ko Yiddish, kalmar Kitsch na nufin duk wani aikin adabi ko zane da bai da tagomashi ga masu mulki ko tajirai ko ya kasance lami ko kwashe-kwashen ayyukan wasu da aka yi a baya, (Wikipidia.org). Adabin Kitsch ya soma watayawa sosai da sosai a kasar Jamus a karni na 19, musamman a kasuwannin birnin Munich a tsakanin 1860 zuwa 1870, inda ake kiran duk wani aikin adabi da ke da arha ko na yayi ko mai karbuwa a tsakanin al’ummar da aka yi domin su ko yake ja a cikin kasuwar sayar da ayyukan adabi da sunan na Kitsch. Shi wannan adabin na Kitsch ba wai na talakawa ba ne kadai, na sababbin matsakaitan tajirai ne da suke da kudin sayen irin wadannan ayyuka, amma karfinsu bai kai na sayen adabin masu gari ba, sun yi haka ne domin a tunaninsu sayen wannan aikin adabin zai sa su tafi kafada-kafada da sarakuna da tajiran Jamus, masu sayen ayyukan adabi na kwarai. Duk da cewa Kitsch ya samu karbuwa a tsakanin jama’a, duk da haka bai wuce adabin kasuwa ko yayi ba ga sauran jama’a, musamman masu sarauta da tajirai, domin kuwa ba a yi aikin da kyau ba ko kuma takardun da aka zayyana hoton ko buga aikin adabin sun kasance na banza, ba su da aminci. Ke nan adabin Kitsch bai wuce adabin Jamus da bai da mazaunin kwarai ba a tsakanin masu mulki da tajirai ko kuma yana magana kan abubuwan da ba su ne aka sa gaba ba a tsakanin al’ummar, ko kuma dai gwanjon adabi ne ko adabi ne da ke kwaikwayon wani adabi, ba tunani ko kirkirar wanda ya samar da shi ba ne ko da kuwa ya samu karbuwa tsakanin wasu gungun mutane, (Cuddon, 1999). Saboda haka kamar yadda muka gani a baya, Kitsch wani nau`in adabi ne da wanzu a kasar Jamus wanda yake nufin duk wani aiki na zane ko aikin adabi wanda masu mulki ko masu kudi ba su yi na`am da shi ba. An samar da wannan adabi ne mai suna Kitsch domin a mai da martani ko ya yi jayayya da ayyukan adabi da aka samar a karni na 18 da na 19 wanda yake ana masa kallo na masu mulkin kasaita da fitattun masu kudi ne. Shi dai wannan salon adabin yana da matukar alaka da adabin da ke tashe ko kuma na yayi, ba wani abu ya sa aka kira shi da haka ba kuwa sai ganin cewa aikin da aka yi na zanen ko aikin adabin ba a yi shi yadda za a iya cewa ya ginu ko tsaru ba. Ke nan adabin Kitsch an samar da shi ne domin matsakaitan masu kudi ko masu mulkin da ba su kai su yi gogayya da wadanda suka yi fice ba, duk da haka su ma wadanda suka yi ficen, ganin karko ko kuma yanayin da wannan adabi ya fita da yadda mutane ke rububinsa ya sanya suka fara saye da karanta shi. Za mu iya cewa adabin Kitsch ya kasance na kasuwa ne kawai domin ganin fasalin yadda aka samar da shi ba mai aminci ba ne, ma`ana kayan da aka yi aiki da su wurin samar da wadannan zane ko ayyukan adabin ba su da inganci, kuma an samar da su ne ganin cewa wadanda suke sayen shi ba su iya sayen manyan ayyukan adabi, wato wannan yana da saukin kudi ga masu sayen shi, kusan kowa zai iya sa kudi ya saye shi Wannan ya sa ake danganta adabin Kitsch, (Wikipedia.org) da duk wani aikin adabi ko zane da aka samar maras kyau, wanda zai iya biya wa mai saye da bukatarsa, ma`ana zai kashe masa kishirwa daga abin da yake so ya gani ko ya karanta, musamman cikin wata sabuwar kama ko siffa, a ayyukan adabin wanda aka kwaikwaya daga wanda ya gabace shi ko suke rayuwa tare. Wannan ne ya sa irin wannan tsari ko fasali ya sha suka daga masana, fitattun daga cikin su kuwa su ne; Gabriel Thuller da wanda ya goyi bayan cewa wannan adabi na Kitsch bai dace da zamanin ba, domin ba gwanaye ke yin sa ba. Haka kuma wani fitaccen masani a fannin zane Georg Wilhelm Friedrich Hegel ya jaddada cewa zane-zanen wannan zamani yana da alaka da wani yanayi na lokacin da aka samar da shi, ba abin damuwa ba ne, in dai ya samu karbuwa daga masu karatu. Adabin Kasuwa Na Larabawa Shi ma adabin Larabci kamar sauran ya sha kwaramniya har zuwa lokacin da aka samar da na zamani wanda yake da alaka da na Yammacin Dauri, (Neo-Classical), wanda ya nemi ya canza fasalin adabin Larabci gaba daya, wato wanda za a ce ya samo kayan aikinsa daga wanda ya gabata, kamar su Maqamatul Hariri da Alfu Laylah, saboda haka su wadannan na zamanin sai ya kasance sun koma ko dai suna samo kayan gininsu daga wadannan ko kuma suna juyar aikin marubuta adabin Yammacin Dauri ne kai tsaye, suna mai da su na Larabci. Marubuta da dama a kasashen Siriya da Lebanon da Egypt sun samar da ayyukansu na adabi daga Maqama, fitattun daga cikinsu akwai Al-Muwayhili da littafinsa na The Hadith of Issa ibn Hisham a zamanin mulkin Ismail a Egypt, wanda wannan littafin shi ne za a iya cewa ya haifar da wani sabon zango a adabin Larabci. Wannan yanayi shi ya ba marubucin nan dan kasar Lebanon,Goergy Zeidan, wanda kirista ne da ya yi hijira zuwa kasar Misira, bayan zanga-zangar da aka yi a Damaskus a 1860 damar fitar da basirarsa a fili sosai. An dai fara buga labarin Ziedan a farkon karni na 18 a cikin jaridar kasar Misira, wato Al-Hilal. Ba wani abu ya sa aka kira ayyukan wadannan mutane da na yayi ko na kasuwa ba sai ganin cewa su ne ayyukan da mutane suka fi sha`awa, saboda irin yadda aka samar da su da harshen da kalmomin da aka yi amfani da su da kuma yadda aka tsara su, sai kuma ficen da marubutan suka yi. Sauran wadanda suka kasance a cikin wannan tsarin sun hada da Khalil Gibran da Mikha`il Na`ima. Amma dai masana da dama na adabin Larabci sun bayyana cewa an fi ganin Littafin Zaynab na Muhammad Husayn Haykal da Adraa Denshawi na Muhammad Tahir Haqqi da kasancewa ayyukan adabi na farko a wannan karni masu kama da ayyukan adabin jama’a ko kasuwa, fiye da wadancan da muka ambata a baya. (dubi karin bayani a Arabic Literature daga Wikipidia: The free encyclopedia). Daga nazarin da aka gudanar an fahimci cewa litattafan adabin yayi ko na jama’a na Larabci sun fi bayyana rayuwar iyali, misali ayyukan Naguib Mahfuz na Cairo Trilogy, inda ya siffanta rayuwar iyali. Adabin Kasuwa Na Onitsha A Nijeriya Kamar yadda wannan fasali na adabin kasuwa ya samu karbuwa da watsuwa a sassan Turai da Amurka da kasashen Larabawa, haka ma inda Turawan suka yi mulkin mallaka fasalin ya samu zaunuwa, ko dai a cikin harshen ‘yan gida ko kuma cikin harshen bakin da suka zo cikin Afirkawa. Misalin da za a iya kawowa a nan shi ne na Adabin Kasuwar Onisha da ya wanzu cikin harshen Ingilishi, masana da dama sun bayyana yadda wannan fasali ya samu ya kuma wanzu . Haka kuma kamar yadda Okoro (2002) ya bayyana, adabin Kasuwar Onisha an yi shi ne a wani zamani a farkon karni na 20 a kasar Inyamurai a Nijeriya da ya kasance, wanda a lokacin an sami al’ummar Igbo da ba su da isasshen ilmin boko, wasu sun kammala Elementare, suka sami aikin malanta ko suka zama masinjoji ko sakatarori a ofisoshin gwamnati a Onisha, sai dai da yawa daga cikinsu sun fahimci ba za su iya rayuwa da irin wannan aiki ba, domin ba albashin kwarai, wasu kuma da ba su sami aikin ba, bayan sun kammala karatu, sai abubuwa suka cunkushe musu, domin wadanda suka yi karatun ma ya suka kare, su kuma masu aikin suna aiki, ga shi karo karatun na da matsala a wannan lokaci. Wannan ya sa wasu da dama suka fantsama cikin kasuwar Onisha ko dai a matsayin ‘yan tireda ko masu koyon sana’ar hannu ta kafinta ko teloli ko magina ko makera. Da yake yawancinsu, sun yi boko to ba su son su zauna haka nan ba abin karatu, ga shi kuma ayyukan adabin Ingilishi da ke makarantu ya fi karfin aljihunsu, sai suka shiga rubuta abin da ya zo ga ransu domin su karanta tsakaninsu; ire-iren wadannan rubuce-rubuce ne aka kira da Adabin Kasuwar Onisha. Ke nan kamar yadda Obiechina (1973) da Okoro (2002) da Malumfashi (2005) suka yi bayani daga nasu binciken ba wani abu ba ne Adabin Kasuwar Onisha sai kananan littatafan nan da aka samu da yawan gaske a kasuwar ta Onisha da wasu sassa na Kudancin Nijeriya a tsakiyar shekarun karni na 20, suka ce, an tsara da shirya da kuma sayar da su domin talakawan Onisha da ba su yi zurfin karatu ba. Wannan adabin na Kasuwar Onitsha, wanda shi ne za a iya kira da wanda ya fara samar da wurin buga litattafai, garin Onitsha dai yana kudancin Nijeriya, mutanen wurin wadanda Igbo ne sun shahara wurin kasuwanci, a wani lokaci ma ana iya cewa kasuwar ta Onitsha ita ce mafi shahara a Afirka. An fara samar da littafin adabi a wannan wuri cikin shekarar 1947, babu wani tsari ko fasali da aka bi domin samar da wadannan litattafan, hasali ma dai an fara samar da su ne domin cike wani gibi da aka samu na karatu da ko rubutu, saboda a lokacin samuwar addinin kirista da `yan mulkin mallaka sun taimaka wurin samar da makaranta a garin Onitsha domin su yi aiki, ko kasuwanci ko kuma su samu wata damar ta ci gaba. Wannan shi ya haifar da masu buga litattafai na bakin hanya ko na kasuwa da suka fara samar da wannan adabi. Wanda za a fara cewa ya fara samar da wadannan litattafan na kasuwar Onitsha ba wai kawai ya yi fice ba ne, a lokacin, mutum ne kuma wanda daga baya ya shahara ta fuskar ilimin boko, wanda kuma yana ma daga cikin wadanda suka wakilci jama`arsu, kuma kwararre wurin hada magunguna (Pharmacist), wato Cyprian Ekwensi, wanda ya tashi daga wallafa littattafan adabin kasuwa ko yayi zuwa wallafa gangariyar adabi. Littafin da aka fara samarwa a lokacin shi ne; Ikolo Wrestler na Cyprian Ekwensi, an samar da shi ne daga tatsuniyoyin Igbo, wanda aka buga a wurin sai da litattafai na Tabansi Bookshop da kuma dayan, When Love Whispers na soyayya. An sake samar da wasu bayan shekara biyu wato; Tragic Niger Tales, mawallafin litattafan wani malamin makaranta ne, yana ba da labarin aure ne ko ma`aurata. Su dai irin wadannan litattafai da aka samar sun yi tashe da suna a duk fadin garin Onitsha da kewaye, musamman a wurin matasa `yan makaranta, maza da mata. Wannan ya sanya wasu marubutan suka biyo baya, don ganin irin amsuwar da wadannan litattafai suka yi. Wannan kuma shi ya sanya aka shiga samar da sababbin masu buga litattafan na bakin hanya, da kuma na cikin kasuwa, shi ya sanya har zuwa shekarar 1960 abin ya habaka, wanda ya sanya masu buga litattafan suka watsu har zuwa garuruwan Aba da Fatakwal da Inugu da sauran manyan garuruwan gabashin Nijeriya. Akwai dalilai da dama da suka sanya aka samu wannan bunkasuwar a garin Onitsha kamar yadda Obiechina (1973) ya bayyana. Wasu daga cikin dalilan kuwa har da kasancewar kasuwar garin Onitsha ta yi fice ba a gabashin Nijeriya ko Najeriyar, kai har fadin Yammacin Afirka. Saboda haka idan aka lura za a ga cewa Adabin Kasuwar Onitsha ya kasance da siffofi da alamu da dama, wadanda suka yi kama da wadanda aka gani a kasar Ingila, ko a Jamus ko na kasar Larabawa, domin dai an yi shi saboda masu karamin karfi su samu abin karantawa, ke nan ba ya da tsada, sannan yana da saurin fahimta, ma`ana harshen da aka yi amfani da shi mai saukin fahimta ne, kuma an yi shi ne musamman saboda talakawa ko wadanda ba su tare da gangariyar adabi. Haka kuma ba su maganar komai sai labaran soyayya da tatsunniyoyi da rayuwar aure da kuma bunkasuwar kasuwanci. Sai dai wannan bai zama abin mamaki ba, domin suna yin la`akari ne da bukatun masu karatun su. Matakan Gane Adabin Kasuwa Abin lura a nan shi ne, irin wannan fasali da Adabin Kasuwar Onisha ya dauka shi ne Adabin Elizabeth a Ingila ko kuma na Kitsch a Jamus, da na Larabawa ya dauka. Ke nan babban matsugunin kowane aikin adabi da aka yi wa lakabi da na kasuwa ko na yayi bai wuce irin fasalin da ya tashi da shi ba, ko dai mai arha ne ko kayan da aka yi amfani da su wajen samar da shi ba su da inganci ko kuma masu yin sa da karanta shi wasu gungun jama’a ne, ba na kowa da kowa ba ne. Gungun mutanen na iya kasancewa masu kudi ko talakawa ko iyayen gari, sannan uwa uba kuma wannan adabi na da lokacin da yake rayuwa, ya kuma mutu, kamar yadda Malumfashi (2005) ya bayyana. Domin gane wannan fasali na adabin kasuwa bari mu dubi adabin Elizabeth na Ingila da kyau, ya dai yi tashensa ne cikin shekara 45, wato daga 1558 zuwa 1603, shi kuma na Kitsch da ke a Jamus, ya rayu ne daga 1860 zuwa 1870, wato shekara 10 ya yi a duniya ko kuma na Onisha daga 1947 zuwa 1975, ya shekara 28 ke nan a raye. Saboda haka, fasalin adabin kasuwa yana zuwa da siffofi da kamannu masu yawa. Sai dai domin takaitawa muna iya cewa shi ne adabin da ake samu a cikin kasuwa, ba wai ana nufin kasuwar dole ta kasance irin wadda muke tunani ba, duk inda jama’a suke hada-hadar saye da sayarwa, shi ake nufi da kasuwa a nan. Idan ana son a gane shi da kyau sai a dube shi da wadannan fasalce-fasalcen : Adabin kasuwa zai iya kasancewa mai saukin karantawa, wato mai jimloli marasa sarkakiya. Haka kuma nahawunsa zai kasance sassauka, ba mai nauyi ba. Haka yawancin wannan adabin yakan kasance bai da yawan shafuka, ma`ana, bai daukar lokaci za a iya karance shi. Ga shi kuma yana da arha, kusan kowa zai iya sanya kudi ya saya ba tare da wani tarnaki ba, (Obiechina, 1973). Jigogin Adabin Kasuwa Sakonni ko kuma jigogin da wadannan ayyuka na adabi suke isar wa sun bambanta ne daga wannan gari zuwa wancan ko kuma daga wannan kasa zuwa waccan, amma dai abu muhimmi shi ne kowane da abin da yake son ya isar ga al’ummar. Alal misali daga nazarin da aka yi wa Adabin Elizabeth da ya wanzu a zamanin sarauniya Elizabeth ta Ingila a tsakanin karni na 16 da na 17, ya shahara ne ta fuskar wasan kwaikwayo da kuma wakoki, sannan kuma kusan yawancin marubutan suna yin rubutunsu ne domin kare martabar masu mulki da kuma tajirai. Wannan ne ma ya sanya tun daga farkon mulkinta, Sarauniya Elizabeth ta kasance tamkar uwar kungiyar, kuma mai ba da taimako ga marubutan, ta yadda kamar yadda muka nuna a wasu lokutta har aiwatar da wasan kwaikwayon ake yi a gabanta. A adabin Larabawa ma musamman kuwa wakokin lokacin jahiliyya, jigonsu bai wuce fadakarwa ta zamantakewa ba, ko kuma rayuwa irin ta yau da kullum ba, sai kuma jigon wakokin yawace-yawace da kuma wakoki na kabilanci da kusan kowace kabila ke da shi. Amma bayan bayyanar Musulunci da wayewar kai sai abin ya canza, domin kuwa litattafan adabin Larabci a lokacin sun fi bayyana rayuwar iyali, misali ayyukan Naguib Mahfuz na Cairo Trilogy, Shi kuwa adabin Onitsha na Nijeriya jigoginsu sai suka sha bamban da na sauran sassan duniya, domin kuwa a lokacin da aka fara samar da shi a 1947, sai ya kasance ya ta’allaka ne wajen ba da labaran soyayya da suka shafi aure da kuma kasuwanci, a sassan wannan yanki na Nijeriya. Ke nan a iya cewa yawancin labaran na Adabin Onisha ba su maganar komai sai labaran soyayya da tatsuniyoyi. Daga baya kuma sun tattauna abubuwa da suka shafi yadda rubuta wasika da yadda ake koyon Ingilishi da kuma tallata haja da makamantansu. Daga binciken da aka gudanar an dai fahimci cewa yawancin jigogi na yawancin Adubban Kasuwa a kowace kasa, suna kasancewa abin da al’ummar wannan wuri ne suka fi so da ko sha’awar gani ko karantawa a daidai lokacin da ake aiwatar shi, ko dai na soyayyar ne ko kuma na kasuwanci, ko rayuwar iyalin ko kuma na masu mulkin, kusan a ce wannan shi ya fi rinjayar masu karanta ko sauraron wannan adabi na wannan yanki. Marubutan Adabin Kasuwa Marubuta wadannan litattafan dai kamar yadda muka nazarci wasu daga cikinsu, shahararru ne a fagen da suke, wasu kuma fitattun malamai ne a makarantun zamanin. Misali, marubuta adabin Elizabeth, wasunsu sun yi fice matuka, marubuta kamar Roger Ascham, wanda yake fitacce kuma shahararren malami ne, domin har sarauniyar Ingilar ma sai da ya koyar da ita a makaranta, an haife shi a shekarar 1515. Sannan ga masana irin su Edmund Spenser da William Shakespeare da Christopher Marlowe da Ben Johnson da Edmund Spencer da John Fletcher da Thomas Kyd da Thomas Middleton da Thomas Nashe da John Webster da John Donne da Philip Sidney, dukkansu fitattun marubuta ne wadanda suka yi tashe a wannan zamani na Elizabeth da kuma bayan wannan zamani. Idan muka dubi marubutan Adabin Kitsch na Jamus, shi ma ya samu fitattun masu zane da rubutu a lokacin, fitattun daga cikinsu kuwa su ne; Gabriel Thuller da Matk A. Cheetham da kuma George Wilhelm Friedrich Hegel. A Adabin kasuwa na Larabawa da muka gani, shi ma ya zo da nasa fitattun marubutan da suka shahara kuma suka samar da litattafai a lokacin, fitattu daga cikinsu akwai Muhammad Husayn Haykal da Muhammad Tahir Haqqi da Naguib Mahfuz da kuma Al-Hamadhani da fitaccen aikinsa na Maqamatil-Hariri da dai sauransu. Haka ma a kasuwar Onisha wanda za a fara cewa ya fara samar da wadannan litattafan na kasuwar Onitsha ba wai kawai ya yi fice ba ne, mutum ne wanda ya shahara ta fuskar ilimin boko daga baya, wato Cyprian Ekwensi, wanda daga baya ya tashi daga wallafa kananan litattafai zuwa manya. MakarantaAdabin Kasuwa Makaranta Ayyukan adabin kasuwa su ma sun bambanta, wasu talakawa ne kadai ke sauraro ko kallo, yayin da wasu kuwa kamar na Elizabeth ya kasance masu sarautar Ingila din suna daga cikin masu yi da sauraron wannan adabi. Sai da ta kai ma wasu ayyukan idan aka yi su, sai a ware wanda za a kai wa sarauniyar, da kuma wanda za a gabatar a bainar jama’a. Saboda haka sai ya kasance daga cikin masu sha’awar wannan aikin; wato ko dai wasan kwaikwkon ko kuma wakoki sun fito daga masarautar Ingilar. Wannan ne ma ya sa marubuta da dama na wannan lokacin sun ji dadin yadda `yan majalisar Sarauniya ke tararryar su. Shi kuwa adabin Kitsch ba wai na talakawa ba ne kadai, na sababbin matsakaitan tajirai ne da suke da kudin sayen irin wadannan ayyuka, amma karfinsu bai kai na sayen adabin masu gari ba, sun yi haka ne domin a tunaninsu sayen wannan aikin adabin zai sa su tafi kafada-kafada da sarakuna da tajiran Jamus, masu sayen ayyukan adabi na kwarai. Shi dai adabin kitsch an samar da shi ne domin matsakaitan masu kudi ko masu mulkin da ba su kai su yi gogayya da wadanda suka yi fice ba, duk da haka su ma wadanda suka yi ficen, ganin karko ko kuma yanayin wannan na Kitsch din ya sanya suka fara sayen shi. Shi kuwa Adabin Kasuwa na Onitsha ya fi shahara ne a wurin matasa `yan makaranta maza da mata, da kuma masu karamin karfi don su samu abin karantawa wanda baya da tsada, ta yadda kowa za iya sa kudi ya saya ba tare da wani tarnaki ba. Kasuwancin Adabin Kasuwa Duk aikin Adabin da ya kasance ana samun shi a wasu wurare da ba na saida litattafan ko aikin adabi ba ne to wannan adabi zai kasance na kasuwa ne ko yayi ko kuma mai tashe ne. Duk adabin da ake bi kasuwa-kasuwa, da shaguna, da wajen `yan tireda, da masu tura kaya a baro, ko wurin `yan kura, kai ko kawai a hanya, ana nemansa don a saya , adabin kasuwa ne, (Malumfashi, 2002). Wannan ya zama gaskiya idan aka yi la’akari da irin wuraren da ake sayar da littattafan zamanin Sarauniyar Ingila Elizabeth Ta Daya, yawancin littattafan ana sayar da samunsu a bakin shagunan da marubutan suka bude don tallata hajarsu, ko dai a cikin birnin London ko kuma kauyukan da ke makwabtaka da shi. An fi ganin su a bakin titi, ‘yan kalilan ne suka samu shiga shagunan sayar da littatafai na zamani. Wasu kuma kamar yadda muka bankado, ana saye da rarraba su ne ta hannu, tsakanin wannan marubuci ko marubuciya zuwa wancan marubuci ko marubuciya. Sai dai za a iya cewa wasu kuma ba ma sayar da su ake yi ba ana aiwatar ko gabatar da su ne a gaban jama’a a lokuttan bukukuwa ko tarurrukan marubuta. Kusan irin wannan fasali ne aka gani a adabin Kistch na Jamus, yaswancin zane-zanen da ayyukan adabin da suka yi tashe a wannan karon an samar da su ne a kasuwar birnin Munich, inda yawancin masu adabin suka rayu. Saboda haka za a iya cewa adabin da zane-zanen duk ‘yan kasuwa ne, don haka a bisa titi ake samu da sayar da su a tsakanin al’ummar wancan zamani. Idan kuma aka lura da tsarin saye da sayarwar littatafan Adabin Kasuwar Onitsha za a fahimci shi ma ya bi irin wannan fasali na baya. Tun da farko dai an yanke wa adabin cibi ne a kasuwar Onitsha, nan yawancin marubutan suka wanzu, sai kuwa wasu sassa na garuruwan Aba da makwabta. Saboda haka yawancin littattafan ana saye da sayar da su ne a wadannan kasuwanni. Ba kuma wani wuri na musamman aka tanadar musu ba, inda ‘yan kasuwar ke saye da sayarwar nan ne littattafan suka samu matsuguni. Samuwar Adabin Kasuwar Kano Daga abubuwan da aka gani a babin da ya gabata ke nan ba abin mamaki ba ne idan aka ci karo da Adabin Kasuwa a Amurka ko Turai ko Rasha ko cikin kasashen Asiya ko Larabawa, kai ko ma ina ne a cikin duniya. Hakan na faruwa ne ganin cewa ai ba kasashen Turawa ko wadanda suka ci gaba ne ke da damar su samar da adabin kasuwa su kadai ba, haka kuma ba dole sai harshen Ingilishi ko wani harshen da ya sami ci gaba kadai ne zai iya samar da shi ba; kowace kasa, kuma kowane irin harshe zai iya samun adabin kasuwa a cikin wani zangon rayuwar adabin. Domin inganta bincike, ya dace mu bi salsala, mu ga yadda aka samar da abin da yawanci ake kira Adabin Kasuwar Kano tsakanin Hausawa. 4.1.1 Rayuwar Farko : 1984-1989 Abin da aka dade ana kira Adabin Kasuwar Kano ya samo asali ne a farkon shekarun 1980, kuma wannan shekaru a kasar Hausa ko Arewacin Nijeriya baki daya, shekaru ne masu tarihi a bangaren samuwar ilmin boko da rubutu. A daidai wannan zangon rayuwa ne daliban UPE, shirin gwamnatin tarayya da aka soma daga 1976 domin ba kowane yaro damar samun ilimin furamare kyauta, suka fara shiga kasuwar rubutu da karatu da rububin abubuwan karantawa, domin daliban farko na wannan shiri sun baro firamare a shekarar 1982, daga wannan lokaci har zuwa 1984, an yaye dalibai har kashi hudu. Saboda haka an samar da sababbin makaranta da suke bukatar abin karantawa. Haka wannan zango ya zo daidai da lokacin da babban kamfanin wallafa da dab’i a kasar Hausa wato NNPC ya soma shiga tasku, ya soma sukurkucewa da neman durkushewa. A daidai wannan lokaci kamfanin NNPC ya daina buga littattafan hira da nishadi, bayan kuma ga dubban matasa da aka yaye daga shirin na UPE sun antayo cike da shaukin irin wadannan littattafai da babu su. Wannan shiri na UPE, duk da cewa bai zaunu da gindinsa ba, amma ya samar da sababbin makaranta a farkon shekarun 1980. Kuma a daidai wannan lokaci sai ga shi tattalin arzikin Nijeriya ya kara inganta, saboda gano man fetur da aka yi, ya kara wa kasar hanyar samun kudaden shiga masu yawa. Bincike kuma ya nuna cewa duk lokacin da irin wannan harka ta kasance haka, wato ga masu ilmi gwargwado, sa’annan ga ‘yan kudi a hannun jama’a, kamar yadda muka gani a fasalin Adabin Kasuwar Kitsch na Jamus, sai ka ga hanyoyin samar da adabi, mai kyau ko maras kyau, suna wadatuwa. Da yake tun can azal akwai kayayyakin rubutu da dab’i gwargwado a kasar Hausa, sai ya ba matasa damar da suka tsunduma cikin wannan harka ta wallafa littattafai ba ji ba gani, kamar yadda Furniss, (2001) ya yi nuni. Sai dai ko kafin shekarar 1984 da littafin Rabin Raina na Talatu Wada Ahmed ya fito kasuwa akwai birbishin rubuce-rubuce na soyayya a kasar Hausa. Idan ba a manta ba a shekarar 1978 kamfanin NNPC ya shirya gasa da ta samar da littattafai a shekarar 1980, kamar su Mallakin Zuciyata na Sulaiman Ibrahim Katsina da So Aljannar Duniya na Hafsat Abdulwaheed da kuma Amadi na Malam Amah na Magaji Dambatta, (Haruna, 2009). Sai dai abin lura shi ne wadannan littatafai daga gasa suka fito, wato sai da aka yi shiri da tsari, haka kuma na hukuma ko kamfani ne, don haka sun biyo tsari da ingancin da ya bambanta su da adabin kasuwa. Ke nan za a iya cewa wadannan littatafai na gasar 1978 sun dai nuna hanya ne na irin adabin da zai biyo bayansu, ba su ne farkon adabin na kasuwa a kasar Hausa ba. A daya bangaren kuma an danganta littafin Rabin Raina na Talatu Wada Ahmed da tushe ko tubalin samuwar adabin kasuwa a kasar Hausa saboda yanayin da ya samu da kuma yadda ya shiga kasuwa. Shi ma ba wai zama aka yi domin assasa wannan fage na adabin kasuwa ba tattare da shi ba. Kamar yadda a karo na farko wadda aka danganta aikinta da Adabin Kasuwar Kano, Talatu ta bayyana wa Mujallar Garkuwa (2000) yadda ta samar da littafin, ta ce ita ba ta san da wani abu wai shi adabin kasuwa ba lokacin da take rubuta littafinta. Ta kara da cewa ta dai rubuta shi ne a lokacin tana makarantar WTC Katsina, tana aji uku, wato wajajen shekarar 1980, ta kuma rubuta shi ne daga gyauron labaran da take ba ‘yan uwanta dalibai lokacin suna makaranta can da dare kafin su yi barci. Bayan ta gama sakandire ne ta fitar da shi ta hanyar aika shi gidan rediyon tarayya Kaduna domin a karanta a shirin Shafa Labari Shuni, amma aka dade ba a karanta shi ba, daga baya ta mika wa wani kamfanin bakin hanya da ake kira Ogwu a Kaduna domin ya buga mata shi. Kamfanin Ogwu ya buga, ya kuma shiga sayar da littafin da ya ga mutane sun dami suna son su karanta. A lokacin da Kamfanin Ogwu ya shiga sayar da littafin, ita Talatu tana Kwalejin Ilmi ta Kafanchan wajen karo ilmi, a can ne wata kawarta ta zo da littafin, tana yi mata bayanin yadda littafin ya yi kasuwa, ita ba ta ma sani ba. Wannan dadin abin da ya faru ya sa ta koma gida ta ji abin da ya auku. Mahaifiyar Talatu ta ba ta kudin da aka samu, ta yi murna kwarai da ganin arzikin da wannan littafi ya jawo mata. Daga wannan lokaci ne ta shiga sake buga littafin, ana watsawa a cikin kasar Hausa, ta yadda abin ya dinga ba ta mamaki na ganin cewa mutane, musamman masu sayar da littatafai daga ko’ina a fadin kasar Hausa ke kira ko yo sakon don Allah ta aika masu da kwafe 500 ko dubu ko dubu biyu ko ma fiye. Fitar wannan littafi da yanayin da ya samu kan sa lokacin bugu da sayarwa da kuma hanyoyin da aka bi aka samar da shi ya nuna wa sauran marubuta cewa ashe akwai wata hanyar rubuta da wallafa littattafai ba dole sai ta bin kamfanonin bugu da wallafa na gwamnati ba. Saboda haka daga samuwar wannan littafi na Rabin Raina a shekarar 1984 za mu iya cewa akalar adabin hira ko kagaggen labari ta soma sauyawa, kuma a iya cewa daga wannan lokacin ne Adabin Kasuwar Kano ya fara ginuwa. Sai dai abin da ke da muhimmanci a nan shi ne ba wai zama aka yi ba domin a tsara da gina wannan fasali na Adabin Kasuwar ta Kano ba, abu ne da ya kasance caccakude, kuma tattare da abubuwa mabambanta da suka hada da : Tun da farko dai akwai matsalar abubuwan karantawa a makarantu da kuma tsakanin sababbin makaranta kamar yadda muka yi bayani. Ga halin da kamfanin NNPC ya shiga daga farkon shekarun 1980 da rashin buga littatafan hira. Ga kuma daruruwan ‘yan makaranta da wadanda suka kammala makarantun, sun kuma rubuta littattafai masu yawa, ba wurin buga su, balle a san da su. Shirin gidan Rediyon Tarayya Kaduna na Shafa Labari Shuni da wasu da dama a gidajen rediyon jihar Kano da Katsina da Sokoto da wasu wurare da dama ya taimaka wajen fito da wadansu daga cikin marubutan da ke boye. Bugun littafin Talatu na bakin kasuwa da yadda ya sami karbuwa ya sanya wasu,kila suka ce su ma bari su gwada bugawa da sayarwa. Saboda haka littattafan da ake ta yayatawa a halin yanzu a matsayin wadanda suka biyo bayan littafin Talatu daga 1984, ba wai shawara suka yi da juna ba, kuma ba su san wani na yin irin wannan aiki ba, kamar yadda bincike ya nuna a halin yanzu. Ke nan jawabin da Malumfashi, (1994) ko wanda Adamu, (1996) da Adamu (2000) suka yi na lissafa littatafan da suka biyo na Talatu kamar haka ba daidai ba ne, sai dai daga littafin Talatu na Rabin Raina sai: Ibrahim Hamza Abdullahi da Soyayya Gamon Jini a 1986. Idris S. Imam da In Da Rai a 1987. Balaraba Ramat da Budurwar Zuciya a 1987. A.M Zaharadden da Kogin Soyayya a 1988. Idan so cuta ne, na Yusuf M. Adamu a 1989. An yi wannan hasashe bisa hujjar da ta nuna cewa babu wani bincike da ya tabbatar da jeruwa da daidaituwar wannan tsari ko kuma wani bayani da ya ce an tattauna tsakanin wadannan mutane na biyo sahun Talatu Wada. Bari mu yi nazarin batun da kyau, tun da farko dai garuruwan marubutan daban-daban suke, Talatu na Kaduna, Ibrahim Hamza na Kano, Idris S. Imam kuwa tun 1984 aka buga littafin nasa ba wai a 1987, Balaraba kuwa ko kafin ta shigar da littafinta na Budurwar Zuciya a layin adabin kasuwa ta fuskar shiga kungiyar Raina Kama, an riga an buga littafin a Zaria,(Gaskiya Corporation a 1984). Haka shi ma Zaharradeen a Kano yake, shi kuwa Yusuf Adamu yana dalibta a Sakkwato ne ya shigo da nasa littafin. Haka kuma daga binciken da aka gudanar an fahimci cewa ko kafin Ibrahim Hamza Abdullahi da littafinsa na Soyayya Gamon Jini a 1986, an samar da Hannunka Mai sanda 1 na Kamarradeeen Imam a 1985, me ya sa ba a shigar da shi cikin layin na farko ba ? Haka kuma a tsakanin 1984 da aka samar da littafin Talatu, ba wai littattafai hudu ne suka yi tashe ba kurum guda 13 ne. Ke nan ba wata kungiya ba ce ko kuma wani taro aka yi ba aka ce a samar da wannan abu da aka kira Adabin Kasuwar Kano daga baya. Shi kuma Malumfashi (1994) da ya kira shi da wannan suna, ya yi haka ne daga abin da ya gani masu kama da juna tsakanin littattafan da irin wadanda aka samar a Onisha kamar yadda ya bayyana daga baya, (Malumfashi, 2004). Kamar yadda muka gani can baya, rayuwar adabi takan shiga cikin wani sauyi ne na wani lokaci, daga baya kuma ta kasance cikin wani tsari na daban, irin wannan shi ne ya faru da abin da aka kira Adabin Kasuwar Kano yanzu. Sai dai wani abu da za a yi la’akari da shi, shi ne, yawancin matasan da suka yi tashe a wancan lokaci a wannan fage ba su yi amfani da kamfanonin dab`i da ake da su don bayyanar da ayyukansu na adabi ga jama’a ba, ba don komi ba kuwa sai don ba wani kamfani da ya damu ya buga ire-iren wadannan litattafai. Ba kuma wai don ba su da kasuwa ko kuma ba su sami karbuwa ba a tsakanin al`umma ba, a`a, a tsakanin shekarun 1978-1982 ba abin da ya fi tashe da karbuwa irin labaran da wasu suke rubutawa, suna aika wa gidajen rediyoyi daban-daban ana karantawa. Ba wani abu ya jawo hakan ba sai ganin litattafan da aka samar daga gasar da aka shirya a 1978 da suka samar da litattafan soyayya na farko da za a iya kira `yan zamani, sun yi tasiri ga rayuwar irin wadannan matasa. Sai dai da alama amfani da aka yi da kafar rediyo, wadda ta sanya kagaggun labarai irin wadannan suka sami martaba, ba wai kawai tsakanin wadanda suka yi boko ba kurum, har ga wadanda aikinsu shi ne sauraron rediyo, ba su iya karatun ba. Bisa wannan tafarkin aka shiga samar da sababbin marubuta, wasu ta hanyar kwaikwayon abin da aka rubuta, suka aika gidajen rediyoyin, wasu kuma ta sake wa tatsunniyoyi da labaran Hausa fasali, wasu ko ta kwaikwayo ko daukar fasalin wasu labaran Ingilishi ko fassara kai-tsaye ko kuma nade fina-finan Indiya da na Turawa zuwa takarda. Cikin dan lokaci kankani sai ga kabod-kabod na gidajen rediyoyin nan sun cika makil, wasu ma suka shiga konawa, wanda ya sa masu rubutun suka shiga guna-guni idan ba a karanta nasu labaran ba. Sai dai kuma wadanda Allah ya tarfa wa garinsu nono daga cikin wadanda aka karanta nasu a gidajen rediyoyin, sai ga shi sun fara samun suna da daukaka. Wannan ya jawo wasiku suka shiga gilmawa zuwa gare su, ana yaba masu, ta haka kuma aka ga cewa ga wata kafa ta samu ta kashe waccan kishirwa ta rashin labaran Hausa da ta addabi matasa, ta yadda a tsakanin shekarar 1984 zuwa 1998 marubuta da sababbin littatafai suka baje kasuwarsu a kasar Hausa. Idan aka yi nazari sosai za a ga ko da Talatu ta bayyana a 1984 a Kaduna, ba a Kadunar ta tsaya ba, domin littattafan sun baje duk fadin kasar Hausa, musamman a Kano da suka dasa rayuwarsu. A Kanon akwai irin littafin Talatu Wada da ya riga ya shiga kasuwa shi ma kafin ma bayyanar na Talatu, wato Wasiyar Babakere na Ibrahim Sale Gumel, a kuma wannan shekara ta 1984, an sami dan uwan na Talatu, wato In Da Rai Da Rabo na Idris S. Imam. Saboda haka ko da Kamarradeen ya shigo da nasa littafin a 1985, ba dole ba ne ya san da abin da Talatu ta yi ko kuma sauran da suka riga nata shiga kasuwa; musamman ganin cewa da ne ga marigayi Abubakar Imam, kuma yana aiki da kamfanin Huda-Huda da ke Zaria, wadanda su ne mawallafansa. Yadda Kano ta shigo cikin harkar da litatattafan da ‘yan Kanon suka samar bai rasa nasaba da suna da tashe da littafin Talatu da na Idris da Ibrahim suka yi a kasuwar Kanon. Littattafai tara ne suka wanzu a wannan lokaci a tsakanin 1986 zuwa 1989. Ga alama kuma su ne suka sanya Kano ta sami karbuwa da Tagomashi a wannan harka ta yadda daga baya Gusau ta shigo sahu, Kanon ta sake bayyana, daga can kuma sai Sakkwato, tare da Yusuf Adamu. Ga dai jerin irin wadannan littattafai da suka kasance na farko ko suka kasance jijiyar da ta gina wannan sabon yanayin rubutu da muke nazari. Daga nazarin wadannan littattafai an fahimci cewa marubuta mata guda biyu suka wanzu, sauran kuma duk maza ne. LAMBA LITTAFI MAWALLAFI SHEKARA 1 Wasiyyar Baba Kere Ibrahim Saleh Gumel 1983 2 In Da Rai da Rabo Idris S. Imam 1984 3 Rabin Raina Talatu Wada Ahmed 1984 4 Hannunka Mai Sanda 1 Kamaruddeen Imam 1985 5 Soyayya Gamon jini Ibrahim Hamza Bici 1986 6 Daji Bakwai Abba Ado Dandago 1987 7 In Da Rai… Idris S. Imam 1987 8 Kogin Soyayya Ahmed Mahmoud Zaharaddeen 1988 9 Turmi Sha Daka Kabiru Ibrahim Yakasai 1988 10 Budurwar Zuciya Balaraba Ramat Yakubu 1989 11 Soyayya Dankon Zumunci Bashir Sanda Gusau 1989 12 Tsalle Daya… Idris S. Imam 1989 13 Idan So Cuta Ne Yusuf M. Adamu 1989 Balaga: 1990 zuwa 1995 Nazarin rayuwar Adabin Kasuwar Kano a zamanin da muka kira na balaga ya fito mana da siffofi mabambanta. Da farko dai lokaci ne da littattafan da suka samu wanzuwa daga shekarar 1984 suka samu karbuwa tsakanin makaranta da masu buga littatafan da kuma masu sayar da su. A daidai wannan zamani ne na shekarar 1990 zuwa 1995 za a ce Adabion Kasuwar Kano ya shiga tashen balaga, mnarubuta da suka yi suna da karbuwa a tsawon shekaru, suka bayyana. Cikin su irin wadannan marubuta akwai Dan Azumi Baba Chediyar ‘Yan Gurasa, wanda ya wallafa littatafai guda 9 a cikin wannan tsakani da kuma Aminu Abdu Na’inna da ya fitar da littatafai guda 6. Akwai kuma irin su Ado Ahmad Gidan Dabino da Bala Anas Babinlata da Badamasi S. Burji da suka wallafa littattafai 4 kowanensu, haka kuma akwai marubuta irin su Balaraba Ramat da Yusuf Lawan Gwazaye da Alkhamees Bature da suka fitar da littattafai bibiyu kowane. Saura kuwa, irin su Ibrahim Mandawari da Ibrahim Sheme da Bashir Sanda, kowane ya fitar da littafi guda. A bangaren mata kuwa, a wannan lokaci ne aka sami fitowar manyan marubuta mata da suka yi tashe a cikin wannan harka da dadewa, marubuta irin su Bilkisu A. Funtua da Hadiza S. Aliyu da Hawwa Aminu da Atika S. Sidi da suka antayo daga shekarar 1994. Abin la’akari dangane da wannan zamani na balaga shi ne, yawancin littattafan da aka samar daga cikin sama da 110 da aka wallafa a wannan tsakani sun fito ne daga taskar kungiyar Raina Kama da muka yi bayani a baya, wadda ke karkashin jagorancin Ado Gidan Dabino. A daidai wannan lokaci za a fahimci cewa wanda ya fi tashe a cikin wannan kungiya shi ne Dan Azumi Baba, wanda ya fito da wani salo na labaran aljannu da dodanni da muridai, sai ko Ado Gidan Dabino da ya dauki fagen soyayya, wanda kuma ya fi kowane daga cikin marubutan shahara, saboda alakarsa da ‘yan jarida da suka yayata shi da shi kuma irin rawar da ya taka wajen tallata kansa da kuma kwazonsa wajen gina labari. Daga jadawalin marubutan da muka samu kai hannu kan su, mun fahimci cewa nan ma maza suka fi shahara a fagen rubutun, domin kuwa mata 12 ne suka tusgo, alhali maza 60 suka wallafa littattafai a wannan zangon Adabin Kasuwar Kanon. Dubi yadda jadawalin littattafan wannan zamani suka kasance daga binciken da aka gudanar a Rataye 7.1. Tsufa Da Hayayyafa: 1996 zuwa 2001 Daga lokacin da kasuwar littatafan Adabin Kasuwar Kano ta yi tashin gwauron zabo daga shekarar 1995 zuwa 1996 amon wannan sabon tsarin rubutu ba inda bai kai ba, wannan ne ya sa harkar ta koma irin ta wani babban kamfani. Kungiyoyin marubuta da suka bullo daga shekarar 1990 kamar su Kungiyar Matasa Marubuta da Kukan Kurciya da Raina Kama da Jigon Hausa duk a cikin birnin Kano da Ruwan Dare a Kaduna da kuma Kungiyar Matasa Marubuta ta Jihar Sakkwato a Sokoto (Adamu, 2006) su ma suka kara wa wannan harka martaba da daukaka a idon mutane. Haka kuma kungiyoyin makaranta irin su Dakata Readers Association da Kabuga Readers Association da Tudun Wada Readers Association da Hotoro-South Readers Association duk a cikin Kano sun agaza wajen tabbatuwar wannan harka. Daga cikin kuma masu sayar da littattafan da suka agaza sosai a daidai wannan lokaci akwai irin su Alhaji Baba na Jakara City Bookshop da Alhaji Musa Danbala na Sauki Bookshop kuma Alhaji Garba Mohammed na Garba Mohammed Bookshop da ke Sabon Gari Kano. Wannan aure na marubuta da makaranta da masu sayar da littattafai da kuma kungiyoyi daban-daban, su ne za a iya cewa kashin bayan wannan fasali na Adabin Kasuwar Kano, wanda ya sanya harkar ta hayayyafa, ta kuma bunkasa fiye da yadda ake tsammani. Wannan ne ya sa aka sami yawancin tarin littattafan adabin Kasuwar Kanon masu yawan gaske da suka kai sama da 400, a daidai wannan zango da muka tattauna. Daga wannan zango ne mata suka fara kunno kai sosai da sosai, domin kuwa an sami marubuta mata sama da 50 . ’Ya’ya Da Jikoki: 2002 zuwa 2008 Littattafan da aka yi wa lakabi da ‘ya’ya da jikoki su ne kagaggun labaran da aka samu daga shekarar 2002 zuwa shekarar 2008. Nazarin da aka yi wa wadannan littatafai an fahimci cewa duk da sauye-sauyen da aka samu na litattafan Adabin Kasuwar Kano a wannan zango, ba a bar fasalin da aka saba ba, wato na yin rubutun bisa tsarin ni na rubuta, ni na gyara, ni na kai inda za a buga mini, ni kuma ke sayarwa da kaina. An dai samu wasu sababbin marubuta ne da irin nasu fasali, sun bullo domin taka rawa irin tasu. Sai dai kamar yadda muka fahimta, wannan ba ya rasa nasaba da ganin cewa tsofaffin marubutan da suka yi tashe a baya, wasu sun watsar da rubutun, ko dai saboda sun yi aure ko kuma yayinsu ya wuce, wasu kuma sun koma wata sana’ar, musamman shirya fina-finai, ga shi kuma bukatar litattafan ba ta kau baki daya ba, wannan ya jaza fitowar sababbin marubuta domin nuna irin tasu fasahar. A wannan zangon kamar yadda muka nazarta, marubuta mata sun sami filin baje kolinsu. Daga cikin littattafan da muka samu kai hannu kan su marubuta mata sama da 76 ne suka yi tashe. Wannan shi ne karon da mata suka yi ambaliya sosai. Haka kuma daga hirar da na yi da makaranta littattafai a wannan zango sun nuna sha’awarsu kan rubuce-rubucen matan, kila wannan shi ya kara sa yawan marubuta matan. A cikin wadannan jerin litattafan na wannan zango, wadda ta fi yawan littattafai ita ce marubuciya Sa’adatu Saminu Kankiya tana da 14 da suka fita a wannan zango, wannan kuma alama ce da ke cewa litattafanta sun fi samun karbuwa ga makaranta. Mai yiwuwa saboda suna dauke da labaran da suka shafi soyayya da aure, wadanda bisa ga nazarin da aka gudanar su ne suka fi tashe a wannan zango. Akwai kuma wasu marubutan mata da suka fi shahara a wannan zango da suka hada da kamar su Saliha Abubakar Zariya da Hadiza Salisu Sharif da Amina Abdullahi Sharada da Zainab Birged da su Sa’adiya Kankiya da Rahmatu Hassan Sanda. Duk da cewa yawancin wadannan sababbin marubuta ne, duk da haka akwai fitattu da suka yi tashe, wasu tun daga haihuwa da kuruciya, ba su kuma daina ba har zuwan ‘ya’yan da jikoki. Cikin irin wannan fasali akwai irin su Rahma A. Majid da kuma su Hafsat A. Sodangi da Zuwaira Isa da Bilkisu Ahmed Funtua, da dai sauransu da dama. Daga cikin maza kuwa, litattafan Nazir Adam Salihi su ne suka fi karbuwa da tashe, ya rubuta guda 13 a cikin wannan zango da muka yi nazari. Shi kuma jigon litattafansa sun sha bamban da na sauran marubutan wannan zamani, domin wani lokaci za ka ga labaran nasa na soyayya ne, amma cikin ban takaici, wata sa’a ma da ban tsoro. Sai dai irin yadda yake wasa da harshe a cikin littattafan nasa ya sa yawancin masu karatu ke biye da shi a kullum. Maje El-Hejeej Hotoro shi ma wani marubucin ne da litattafansa da kuma tauraruwarsa, musamman a wannan zango suka yi tashe. Shi ma din yakan yi amfani da jigon soyayya ko kuma jigon ban tsoron da jan hankali. A daidai kuma cikin wannan zango ne aka soma ganin bullar sabon tsarin rubutun Adabin Kasuwar Kanon. Da farko dai an sami marubutan da suka canza akalar rubutun nasu domin ya dace da zamani musamman ganin cewa an sha suka da takaddama kan yawaitar rubuce-rubuce kan soyayya da aure. Ire-iren wadannan marubuta sun hada da Bala Anas Babinlata da Ibrahim Sheme da Sakina A. Aminu da Rahma A. Majid da Saliha Abubakar Abdullahi da sauransu da dama. Daga nazarin da aka yi, an fahimci cewa yawancin wadannan marubuta ko dai ilminsu na zamani ne da suka nisa a ciki ya sa littattafan nasu suka yi armashi; wato kamar Ibrahim Sheme da Rahma Majid da suka nazarcin adabin duniya daban-daban, da yake sun yi digiri, Ibrahim Sheme har digiri na biyu ya yi, ko kuma sun dai tsara littattafan ne domin su dan sha bamban da wadanda aka saba ji da gani a wannan zango bisa sani, domin sun ga yadda aka dade ana ta kai-kawo game da neman sauyi, wato kamar su Babinlata da Rahma da Saliha da Abdullahi da Mukhtar Yaron Malam. Duka dai alamu ne da ke nuni da cewa sabon yanka rake na Adabin Kasuwar Kano ya shigo kasuwa. Baya ga wannan kuma ga gasar kaga littatafai da ta kunno kai, musamman ta Bashir Karaye da aka fara a shekarar 2007, wadda ta ba da dama aka sake daga martabar rubutun da kuma marubutan wannan zango. A nan ana maganar irin su Ibrahim Sheme da Lawan Barista da Maje El-Hajeej da suka cinye gasar rubutun a cikin wannan zango. Siffofin Adabin Kasuwar Kano Da yake ana tariyar abin da ya wuce ne game da wannan fage na Adabin Kasuwar Kano, ta yaya za a iya gane aikin adabin da za a ce na Kasuwar Kano ne idan an gan shi, ko kuma wadanne siffofi ne za a ce su ne na Adabin Kasuwar Kano? Amsar na da sauki ganin cewa an riga an yi shimfida game da Adabin Kasuwa na bai daya a cikin babi na uku. Saboda haka abin da aka yi a nan shi ne a fitar da kamannun da su ne za a iya gani a ce wannan na daga cikin siffofin Adabin Kasuwar Kano. Haka kuma yin hakan ya zo da sauki domin daga cikin siffofi na bai daya da aka gani can baya game da adabin kasuwa da manazarta suka ayyana, an fahimci cewa yana dauke da manyan siffofi guda hudu: Adabi ne da ke yin tashe a wani zamani daga baya ya kau. Adabi ne da yake gudana tsakanin wasu gungun mutane kurum ba kowa da kowa ba. Adabi ne na kasuwa ko na yayi. Adabi ne da ake alakanta shi da wani wuri ko gari ko zamani ko yanayin da ya sami kansa. Idan muka dubi littatafan adabin da ake yi wa lakabi da Adabin Kasuwar Kano kamar yadda muka zayyana a baya, za a ga cewa sun shiga cikin sahun adabin kasuwa kamar yadda suke zayyane a sama. Tun da farko wannan harka ta samo asali ne a wani ayyanannen lokaci, wato daga farkon shekarun 1980, musamman a tsakanin shekarar 1983 zuwa 1984 ya zuwa farkon karni na 21, inda daga lokacin ya fara salamcewa, domin harkar fim ta sha gabansa. Saboda haka shi ma kamar sauran ayyukan adabin kasuwa irinsa, ya samu wani lokacin da ya fara da kuma lokacin da ya girma, kuma zai kasance ya koma cikin taskar tarihi a cikin wani lokaci mai zuwa. A halin yanzu dai an samu sama da shekara 25 ana aiwatar da wannan tsari na adabin kasuwa a kasar Hausa Haka kuma adabi ne na gungun matasa, ba na kowa da kowa ba, yawancin masu yin sa da karanta shi ba su wuce ‘yan shekara 18 zuwa 35 ba. Idan aka dubi samuwar wannan fasalin rubutu daga 1983, marubuta biyu ne daga cikin 13 da ake da su, suka haye shekara 25, wato Balaraba Ramat da Kamarradeen Imam, saura duk ‘yan kasa da 25 ne. Sa’annan kuma adabi ne na ‘talakawa’, wato wadanda suke da karamin karfi, ba dole sai masu kudi ko tajirai za su iya sayen sa ba, kamar yadda yake a gangariyar adabi. Da yake kuma adabin talakawa ne, shi kuma adabin talakawa yana zuwa da nasa siffofin na daban; daga ciki zai kasance mai saukin karantawa, wato mai jimloli marasa sarkakiya. Haka kuma nahawunsu zai kasance sassauka, ba nannauya ba. Ke nan wannan adabin yakan kasance bai da yawan shafi, ma`ana, bai daukar lokaci za a iya karance shi. Idan aka dubi nazarin da aka yi a sama za a ga cewa wannan fasali ya fito fili. Yawancin littattafan sun kasance masu saukin karantawa ga dan firamare ko sakandare, haka ma wanda ya yaki jahilci. Idan aka koma kan batun cewa adabin kasuwa ana alakanta shi da wani wuri ko zamani ko gari ko yanayi, za mu iya cewa lallai haka abin ya faru da Adabin Kasuwar Kano. Mun dai ga cewa zamanin Sarauniya Elizabeth ya haifar da Adabin Kasuwar Elizabeth a Ingila, na Kitsch ya haifar da Adabin Kasuwar Kitsch a Jamus, kasuwar Onitsha ta haifar da Adabin Kasuwar Onitsha a Nijeriya. Saboda haka sanya wa Adabin Kasuwar Kano sunan na kasuwar Kano ya danganta ne da ganin cewa Kano tana da fitacciyar kasuwa wadda daga ko`ina ana zuwa cin wannan kasuwa. Kamar yadda kasuwar Onitsha ta yi fice a duk fadin Afrika, ta yadda duk wani littafi da aka wallafa a wannan bangare za a iya samun shi a wannan kasuwa ya ba da damar a sa masa wannan suna. Ko da kuma aka gama cin kasuwar a kasar Inyamurai, a tsakanin shekarun 1947 zuwa 1969, kasuwar ta watse a 1975, sai aka yi wa wannan rayuwa da abin da ta haifar lakabi da Adabin Kasuwar Onitsha, (Okoro, 2002). Saboda haka ba sai an fada ba, tun da Kano birni ne na kasuwanci, sa wa adabin kasuwa lakabin Kano, an yi shi ne da sani da kuma amincewar haka abin yake a tarihin adabin duniya. Kasuwanci dai a birnin Kano ya sami gindin zama sama da shekaru dubu da suka wuce. Birnin Kano ya kasance matattarar kasuwanci da dadewa tsakanin kasashen Hausa, tun zamanin cinikin bayi. Saboda haka ko da wadannan litattafai suka soma bubbugowa daga Kano da Kaduna, Kano suka yada zango. Kuma daga shekarar 1984 da Talatu Wada ta fiddo littafinta, wanda shi ne ya yi wa wannan fasali mazaunin farko, Kano aka kawo shi domin sayarwa ga sassan duniya a can kuma ya samu karbuwa sosai. Daga wannan lokaci ne Kanawa da ke bin wannan sana’a suka shiga sayar da litattafan, suna sarar duk wani littafi da ya fito, su dinga biyan marubuta a hankali. Wasu masu sayar da litattafan suka shiga buga litattafan da kansu, wato su bayyana wa marubuci irin labarin da suke so a rubuta, su kuma sa kudi su buga, su rarrabar, su sami riba, (Adamu, 1998 da 2002). Shafuka Rashin yawan shafuka kamar yadda bincike ya nuna bai rasa nasaba da dalilai da dama. Na farko, tunanin yawancin marubutan irin wadannan littatafai bai cika cokali ba, don haka ko sun tashi yin tunani mai zurfi don su tsawaita labarin, sai ka ga zaren ya tsinke, sun kuge ga shafuka 40 zuwa 80. Daga baya ne dabarar tsinka labaran ta shigo ga marubutan, domin su ninka ribar da suke samu. Wannan shi ya haifar da littafi na daya da na biyu, ko uku, ko ma fiye, kamar yadda aka sami irin wannan siffa a ayyukan adabin Onitsha. Kila abin da wani zai tambaya shi ne me ya sa littattafan za su kasance marasa yawan shafi? Kamar yadda bincike ya nuna, yawancin marubutan da suka yi tashe daga 1984 zuwa 1991, an fahimci cewa ba su yi zurfi a ilmin zamani ba. Alal misali Ado Gidan Dabino, bai yi karatun zamanin ba, makarantar dare ya yi, daga baya ne ya wuce zuwa karo ilmi, shi ma bayan ya zama wani abu a cikin fagen rubuta irin wadannan littattafai. Su kuwa sauran matan da suka shahara a wannan fage ba su wuce karatun firamare da sakandare ba, irin su Zuwaira Isa da Bilkisu Ahmed Funtua, sun isa misali. Wasu kuma sun yi tishin karatun ne bayan sun yi shekaru da gama firamare, har an yi musu aure, suka koma fagen rubutun. Irin su Zuwaira Machika, sun zama misali. Saboda haka duk yadda irin wadannan marubuta ke son su tsawaita littatafan, sai a ga abin ya faskara. Sa’annan kuma uwa-uba, siffar irin wadannan littatafai ke nan, ba a yi su domin yawan shafuka ba. Yanayin Bugu Duk adabin da bai da wani kamfani takamaimai ko wurin dab`i da hukuma ta san da shi, ko kuma bai bin tsari da doka na dab`i kamar yadda aka tanada, to wannan adabi, na kasuwa ne. Duk wani adabi da ba a san shi a manhajar karatu ta firamare ko sakandire ko wani mataki na karatu daban da wadannan ba, ko kuma ya bi tsarin shigar da shi cikin manhajar ba, wato ta bin doka, to wannan adabi na kasuwa ne. Idan haka ne to da wuya irin wadannan littattafai su kasance ba na kasuwa ba. Wannan ya zama haka ne ganin cewa ana buga su ne a bakin titi ko wurin buga littattafai da ke makare a cikin kasuwa. Haka kuma ba sa shiga cikin manhajar karatu kamar yadda hukuma ta tsara domin da ma ba gangariyar ba ne. Idan har aka ga ana karanta su a sakandare ko jami’a to wani shiri ne tsakanin marubutan da malamai, ba wai hukumomin makarantun sun san da shirin ba. Ba wannan ba ma, hatta wadanda ke wallafa littattafan ba suna wallafa su ne domin su yi karko ne ba, a dai buga da takarda mafi sauki, da bango mafi arha, a kuma injuna marasa caji da tsada. Domin fahimtar wannan siffa sosai, ya dace a gane cewa takarda kala biyu ce ake amfani da ita wajen wallafa ire-iren wadannan littattafai; akwai news print da kuma bond. Ita newsprint tun asali ita ce ake amfani da ita, domin ta fi arha. A daidai lokacin da aka soma wannan harka, da naira dari biyar zuwa dubu daya za a iya sayen takardar da za a buga kwafe dubu zuwa dubu biyu, Saboda haka duk tsadar littafin bai wuce naira 5 zuwa 10 daga haihuwa zuwa kuruciya, a kuma samu sami riba in an sayar. Hatta bangon littafin ba da takardar kwarai ake buga shi ba, saboda a rage tsadarsa. Baya ga wannan masu bugawar ba su da kayan aiki na kwarai da suka hada da injuna da tawada da makamantan su. Ke nan duk wani littafin da ya sami kan sa a cikin irin wannan hali, to za a ga bugun zai kasance ba na kwarai ne ba, kamar dai yadda muka ga haka game da littattafan Grub Street a kasar Ingila da Kitsch a Jamus. Sako Ko Jigo Sakon da litattafan Adabin Ksauwar Kano ke isar wa a fili suke, domin kamar yadda (Adamu, 2006) ke cewa, kusan marubuta na farkon-farkon, wato irin su Talatu Wada Ahmed mai (Rabin Raina) da sauran su, soyayya ce suka tanada a cikin littattafan nasu, ba don komi ba sai don su ne ke shere masu karatu. Shi ya sa Adamu (2006) yake nuni da cewa kusan tun daga bangon litattafan za a fahimci jigonsu, saboda daga bangayen, jigon zai bayyana cewa wadannn litattafai na soyayya ne, domin ba abin da za ka gani daga ‘In Da So Da Kauna’, sai ‘Dace Da Masoyi’, sai ‘Kwabon Masoyi’, sai ‘So Tsunstu’, sai ‘Ruwan Soyayyar Zuciya’, sai ‘Kibiyar Soyayya’ da dai sauransu da dama masu dauke da irin wadannan sunayen. Da tafiya ta yi tafiya sai aka fara samun wasu masu magana kan auren da yanayin auren Hausawa da matsalolin da ke tattare da su. Ya zuwa shekarar 2002 zuwa 2008 sai ya kasance sakonnin ko jigogin litattafan sun canza fasali gaba daya, domin kuwa sama da kashi casa`in da takwas na litattafan sai suka koma ba su maganar komai sai labaran soyayya, kamar dai yadda suka faro daga farko. Sannan kuma daga abin da masu karatu suka fada game da sakonni ko jigogin litattafan sai aka fahimci cewa soyayya da rayuwar zaman aure su suka fi tashe, sai kuma zamantakewar yau da kullum, (Bashir, 2009). Sai dai domin a fidda wannan fasali fili, ya dace mu nazarci sakonni ko jigogin wadannan littattafai sosai. Tuni dai (Adamu, 2006) ya taba gudanar da makamancin wannan aiki, sai dai littattafan da ya nazarta ba su wuce 463 ba. Wannan nazari ya dora bisa wancan, an samu ganin cewa sakonnin da ke cikin litattafai sama da 712 da aka yi nazari sun kasance mabambanta, duk da haka dai jigon soyayya shi ne kan gaba. Ga yadda jadawalin ya kasance. JIGO ADADIN LITATTAFAI Soyayya 250 Rayuwar Aure 62 Zamantakewa 164 Rikici 30 Kishi 27 Yaudara 25 Biyayyar Iyaye 12 Ban Dariya 8 Siyasa 12 Hakuri 20 Wadanda Ba A Tantance Ba 102 Kamar yadda Adamu (2006) ya nuna daga nasa binciken kimanin kashi 35 ne kadai suke da jigon Soyayya, sauran kashi 65 kuwa suna magana ne kan wasu jigogin na daban, amma duk da haka wai manazarta na ta sukar marubutan, da cewa sun ta’allaka ne kan jigon soyayya. Amma daga nawa binciken, ana iya ganin cewa kaso mafi tsoka daga cikin littatafan da aka nazarta kusan 712 na soyayya sama da 250 ne, sai sauran jigogin da marubutan sukan tabo. Daga binciken da aka gudanar sauran jigogin da wadannan marubutan sukan tabo sun hada da Rayuwar aure (misali, Matsalar Mu Ce na Fauziyya D. Sulaiman,) da Kishi, (misali, Bakin Kishi na Muhammad Lawan Barista) da Yaudara, (misali, Mayaudariya na Abubakar Umar Mani) da Rayuwar Duniya, ( misali, Zaman Farko na Ibrahim Birniwa) da Hakuri, (misali, Mahakurci, na Sa’adatu Saminu Kankiya) da Ban Dariya, (misali, Namijin Kunama na Balarabe Abdullahi Yola) da Biyayyar Iyaye, (misali ,Tsakanin Da da Mahaifi na Sanusi Hashim,) da Rikici, (misali, Sadauki Diknar na Abdulkadir Mu’azu Isa,) da Tsaro, (misali, An Yanka Ta Tashi na Bala Anas Babinlata da dai sauran su. Su ma idan aka yi musu nazarin kwakkwafi za a ga cewa wasu daga cikin su na soyayyar ne kodayake ba kai tsaye ba, amma dai suna da alaka da soyayyar, musamman wadanda suka shafi rayuwar aure da kishi da makamantan su. Bincike ya nuna cewa an samu wadannan canje-canje ne dangane da fasalce-fasalcen wadannan littattafai da muke magana kai daga mabambantan dalilai. A cikin shekara bakwai da fara wannan harkar adabi, wato lokacin da shekarar 1991 ke karatowa, abubuwan sun bunkasa sosai a wannan fage. Wannan sabon salon rubutu ya cika da batsewa, ya kuma fantsama a ko’ina a kasar Hausa, musamman wurin mata da matasa. Haka kuma ya kasance rubutun ya tashi daga kagawa da aka fara gani a rubucen-rubucen farko, sai ya koma kwashewa ko gamade. Marubuta litattafan sai suka koma kwaso kayan cikin adabin daga fina-finan Indiya da majigin Turawa da Larabawa da kuma litattafan soyayyar Turawa suna mayar da su nasu. Daga shekarar 1991, lokacin da su Ado Gidan Dabino suka yi ruwa, suka yi tsaki, harkar buga litattafan ta koma tamkar kamfani, kungiyoyi daban-daban suka shiga bullowa, tare da shugabanni da mambobi da kuma masu tallata litattafan da suke wallafawa. Wannan kamar yadda muka yi bayani a baya ya taimaka sosai wajen tabbatuwar wannan harka, wanda ya sa aka samar da litattafai sama da 1,860 zuwa shekarar 2007. (Furniss, 2007). Bayan samun gindin zama da Adabin Kasuwar Kano ya yi, har ta kai ga sun kakkafa kungiyoyi domin tafiyar da harkokin rubuce-rubucensu, sai kuma sauran jama`ar gari suka bi sahu. Manazarta da `yan jarida da kuma sauran mutane suka fara tofa albarkacin bakinsu kan yanaye-yanayen wannan adabi. Wasu suke yabawa, yayin da wasu kuma sun nuna irin yadda rubuce-rubucen suka dagule, musamman idan aka hada su da gangariyar aikin adabi da suka gabata. Da dama mutane sun nuna rashin jin dadinsu na yadda batsa da mugayen kalamai suka fara gurbata al`adun Hausawa daga cikin rubuce-rubucen Adabin Kasuwar Kano. Su kuma marubutan a koyaushe kokarin kare kansu suke yi daga zarge-zargen da ake masu. Sukan nuna cewa jigon soyayya da suka dauka don gina ayyukansu, suna yi ne saboda ya dace da zamani ne. Wannaan ya sanya a lokacin idan mutum ya duba kasuwannin litattafai na Hausa ba abin da zai tsinkaya sai dalar litattafai daban-daban na soyayya, irinsu; In Da Rai… ko Rabin Raina ko Budurwar Zuciya ko Furen Soyayya ko Idan So Cuta Ne. Akwai kuma irin su Garin Masoyi da Marurun Soyayya da So Marurun Zuciya da Duniya Bautar Mata da sauransu dai da dama. Masu Sayarwa Kamar kowane irin tsarin adabin kasuwa, Adabin Kasuwar Kano ya zo da nasa fasalin sayar da littattafan. Sai dai shi ma kamar sauran ana sayar da littatafan ne a manyan kasuwannin kasar Hausa da suka hada da Kano da Kaduna da Jos da Sakkwato da Zaria da Gusau da Gombe da Bauchi da Minna da Katsina da sauransu da dama. Wadanda suka taimaka a wannan fage kamar yadda Adamu (2002) ya bayyana su ne dillalai ko masu bugawa da sayarwa a kasuwannin Kano da sauran sassan kasar Hausa, musamman da yake a wancan lokaci ba wani shago da ake da shi da ke tallata littatafan Hausa kurum. A birnin Kano, inda nan ne harkar ta zaunu sosai akwai irin su Alhaji Baba, mai Jakara City Bookshop da Alhaji Musa Danbala, mai Sauki Bookshop da Alhaji Garba Mohammed, mai Garba Mohammed Bookshop. Da farko dai wadannan shaguna suna dillancin littatafan ne da masu rubutawa ke kawo musu su sayar, amma daga baya sai suka koma masu wallafawa da bugawa su da kansu. Za su sayi littafi hannun mai shi ko kuma su sayi wanda ba a buga ba, su su buga suna sayarwa. Daga nan Kano harkar ta koma sauran biranen, su ma da manyan dillalansu da suka hada da irin su Alhaji Abdullah a kasuwar Sakkwato da kuma shagunan littattafai irin su Anti Bilki Bookshop a Funtua da makamantansu da dama. Haka wannan harkar ta ci gaba da wanzuwa har ta kai an samar da shaguna da suke ba sayarwa kurum suke yi ba suna bayar da hayar wadannan littatafai ga wadanda ba su da karfin sayen littattafan ko kuma ba su son su tara su jibgi a gida. Masu Karatu Masu karatun wadannan litattafan kamar yadda muka gani a can baya mafi yawa matasa ne. Sai dai domin mu fahimci inda aka fito dangane da wannan bangare na bincike, na ga ya dace a bi diddigin game tunanin masu karanta wadannan littatafai. Hanyar da aka bi domin yin haka, ita ce ta rarraba takardun neman bayanai domin a ji daga bakin masu karatu game da abubuwa da dama da suka shafi wannan harka. Daga cikin takardun neman bayanai sama da 400 da aka rarraba a sassan garuruwan kasar Hausa, kamar Katsina da Kano da Kaduna da Sakkwato da Zariya da Gombe da Dutse da kuma Bauchi, an samu guda 350 da suka dawo hannu. An yi amfani da wadannan takardun bayanai domin gane matsayin makaranta wadannan littattafai. Ga dai fasalin rabe-raben takardun neman bayanin da aka samu. JADAWALI NA FARKO: BAYANAI DANGANE DA SHEKARU SHEKARA WADANDA SUKA MAIDO ADADI 1-20 40 Kashi 2 21-40 287 Kashi 97 41-60 23 Kashi 1 JIMILLA 350 Kashi 100 Kamar yadda muka gani a sama, mafi yawan masu karanta wadannan litattafan da suka amsa tambayoyin neman bayani shekarunsu sun kama daga shekara 21 zuwa shekara 40. Sai kashi daya wadanda shekarunsu suka kama daga shekara 41 zuwa shekara 60. sai sauran da shekarunsu ya kama daga 1 zuwa ashirin. JADAWALI NA BIYU: BAYANAI DANGANE DA ADDINI ADDINI WADANDA SUKA MAIDO ADADI MUSULUNCI 350 Kashi 100 KIRISTANCI 0 0 JIMILLA 350 Kashi 100 Haka kuma an dubi addinan wadanda suka maido bayanan daga wadanda suke karanta wadannan litattafan. Su kuma kashi 100 cikin dari dukkan su musulmi ne. Wannan shi ma bai zama abin mamaki ba, musamman ganin cewa yawancin garuruwan da aka rarraba takardun na muslmi ne. JADAWALI NA UKU: BAYANAI DANGANE DA KABILA KABILA WADANDA SUKA MAIDO ADADI HAUSA/ FULANI 350 Kashi 100 SAURAN KABILU - Kashi 0 JIMILLA 350 Kashi 100 Daga takardun da muka samu karba na neman bayanai mun fahimci cewa mafi yawan wadanda suka yi mana bayanan Hausawa da Fulani ne, domin kamar yadda ya zo a teburi na uku, kashi dari na daga masu karanta litattafan Hausawa da Fulanin ne. Wannan ko bai rasa nasaba da cewa Hausawa da Fulani ke zaune inda aka rarraba wadannan takardun neman bayanai. Sannnan kamar yadda ya zo a teburi na hudu a kasa, mai nuna matakin ilimin wadanda suka amsa tambayoyin namu, mun ga cewa matakin ilminsu bai yi zurfi ba, domin sun kama daga matakin sakandare, mai kashi 27 cikin 100 ne, zuwa matakin karatun difloma ko NCE, ko kuma wata babbar shedar karatu, masu kashi 70 cikin 100. Sai dai akwai wadanda suka yi digiri masu rabin kashi da kuma wadanda suka yaki jahilci masu kashi daya. Sai kuma masu ilmin addini kurum, masu kashi daya su ma. JADAWALI NA HUDU: BAYANAI DANGANE DA MATAKIN ILIMI MATAKIN ILIMI WADANDA SUKA MAIDO ADADI ILIMIN ADDINI 14 Rabin Kashi ILIMIN SAKANDIRE 120 Kashi 27.1 N.C.E/DIFLOMA 148 Kashi 70 DIGIRI 10 Rabin Kashi YAKI DA JAHILCI 58 Kashi 1 JIMILLA 350 Kashi 100 Dangane da garuruwan da wadanda suka amsa tambayoyin suka fito, wannan binciken ya nuna cewa Katsina (da kashi 40) da Kano (da kashi 34), nan ne aka samu yawancin amsar tambayoyin bayanan da aka nema. Katsina dai ba abin mamaki ba ne, domin mai binciken a nan yake da zama, ke nan ana iya samun takardun neman bayanin da suka dawo masu yawa a nan. Kano dama can ake sayar da litattafan, saboda haka ba abin mamaki ba ne don an samu amsar tambayoyi da dama daga can. Haka akwai sauran sassan garuruwan da aka dawo da amsoshi kamar yadda yake a teburi na kasa. JADAWALI NA BIYAR: BAYANAI DANGANE DA GARI GARI WADANDA SUKA MAIDO ADADI KATSINA 142 Kashi 40 KANO 92 Kashi 34 GUMEL 2 Rabin Kashi SOKOTO 40 Kashi 10 BAUCI 2 Rabin Kashi GOMBE 2 Rabin Kashi ZARIYA 25 Kashi 5 KADUNA 45 Kashi 10 JIMILLA 350 100 JADAWALI NA SHIDA: BAYANAI DANGANE DA JINSI JINSI WADANDA SUKA MAIDO ADADI Namiji 112 Kashi 30 Mace 178 Kashi 65 Ba Jinsi 60 Kashi 5 JIMILLA 350 Kashi 100 Dangane da jinsin wadanda suka mayar da takardu kuwa, daga binciken da aka gudanar a teburi na 6, ya nuna cewa kashi 65 daga cikin wadanda suka mayar da bayanai mata ne, sai mai bi musu, maza, masu kashi 30. Akwai kuma wadanda ba su bayyana jinsinsu ba. JADAWALI NA BAKWAI: BAYANAI DANGANE DA SUNAN ADABIN KASUWAR KANO SHEKARA WADANDA SUKA MAIDO ADADI 1-20 20 Kashi 1 21-40 320 Kashi 98 41-60 10 Kashi 1 JIMILLA 350 Kashi 100% Daga binciken da aka yi sama da kashi 98 sun san da cewar ana kiran wadananan litattafan da litattafan soyayya ko kuma Adabin Kasuwar Kano, kalilan ne daga ciki ba su sani ba, su ma kuma din daga abin da aka kalato, rashin sanin nasu ba ya rasa nasaba da cewar ko dai ba su mai da hankali ba ne ko kuma suna yin karatun ne ba tare da sanin ana kiran su da wani suna ba, face Hadisan Kano da suka ce suna jin ana kiran su da shi. Yawancin wadanda suka san da sunan littattafan Littattafan Soyayya ko Adabin Kasuwar Kano, matasa ne masu shekara 21 zuwa 40 kamar yadda yake a teburin na bakwai. Mafi rinjaye daga masu karatun da suka san da wadannan sunaye da ake kiran wadannan littattafai da su suna karanta littatafan domin. kusan kashi 70 na wadanda aka nemi bayanansu, suna karanta litattafan musamman matasa, kamar yadda muka gani a teburi na uku. Sai dai wasu daga cikin wadannan kashi din suna ganin cewa sunan da ake kiran wadannan littattafai da shi bai dace da shi ba. Kusan kamar kashi uku na daga wannan kason suna ganin bai dace a rinka kiransu da Adabin Kasuwar Kano ba, sai dai a kira su da litattafan soyayya ko kuma a canza masu wani sunan. JADAWALIU NA TAKWAS: BAYANAI KAN INDA AKE SAYEN LITATTAFAN INDA AKE SAYEN LITATTAFAN WADANDA SUKA MAIDO ADADI KASUWA 345 Kashi 99.9 KANTUNAN SAIDA LITATTAFAI 5 ½ JIMILLA 350 Kashi 100 Sannan dangane da kudaden da ake sayen litattafan ma bayanai sun zo daidai, domin akasarin amsoshin da aka maido sun nuna cewa kudin litattafan sun kama daga Naira 40 zuwa Naira 200. Dangane da maganar ba da hayar wadannan litattafan, su ma din kusan kaso 80 cikin 100 na wadanda suka amsa tambayoyin sun tabbatar da cewa sun san ana ba da hayar wadannan litattafai. Kashi kamar ishirin ne ba su sani ba, su ma din watakila don sayen litattafan kawai suke yi, ba su mai da hankali ga lura da cewar ana ba da hayar ba. JADAWALI NA TARA: BAYANAI DANGANE DA KO ANA KARUWA DA KARATUN LITATTAFAN Sama da kashi 85 cikin 100 da suka amsa tambayoyin sun nuna cewar ba su karuwa da komai daga karanta wadannan litattafan, suka ci gaba da cewar suna karanta litattfan ne kawai ko dai don rashin abin yi ne ko kuma don nishadi. Kaso kamar 15 cikin 100 su ne suka ce suna karuwa da sakonnin littattafan, kuma daga cikinsu mafi yawanci mata ne suka ce suna karuwar da ko dai zaman aure ko kuma soyayya ko mallake miji da dai sauransu. Sannan kuma ko a maganar darussan da ke cikin litattafan maganar ba ta canza zane ba, saboda abin da aka zakulo, masu karatun sun nuna cewa sun fi sha’awar daga na soyayya, sai zamantakewar aure ko rayuwar jama’a da dai sauransu. Ga dai yadda fasalin yake a teburi na kasa. ANA KARUWA DA KARATUN LITATTAFAN WADANDA SUKA MAIDO ADADI EH 15 15 A’A 335 85 JIMILLA 350 Kashi 100 Dangane da masu sana’ar ta ko dai rubuta litattafan ko kuma buga su, su ma babu abin da suke cewa da ya wuce sun shiga harkar ne don bunkasa adabi, sai kuma don neman kudi. Wasu sun nuna cewar lallai harkar akwai riba, amma wasu sun nuna cewa babu wata riba sai dai a yi don bunkasar adabin kawai. Haka kuma kan maganar matsalolin da suke fuskanta wajen rubutun, maganar kudi ita ce gaba, sai kuma kayan aiki na dab’i da sauransu.

No comments:

Post a Comment